Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Ambaliyar Ruwa Na Cigaba Da Janyo Asarar Rayuka A Kebbi

by Tayo Adelaja
September 16, 2017
in RAHOTANNI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk, Birnin Kebbi

Wasu rahotanni sun bayyana cewar matsalar ambaliyar ruwa a Jihar Kebbi na ci gaba da zamarwa al’umma barazana ta rasa gidaje da dukiyoyi miliyoyin a kowace shekara, har ila yau, al’umma sun zuba igo domin ganin Gwamatin Tarayya da ta Jiha sun magance balahirar amma lamarin shiru.

Da yawan wadanda bala’in ya rutsa da su suna zaune a makarantun firamarai da sakandarai na garuruwan su. Yayin da a wasu lokutan suke samun tallafi daga hukumomi.

Rahotannin da ke fitowa daga Dolekaina da ke karamar hukumar Dandi, an tabbatar da cewar ambaliyar Ruwa ta mamaye gidajen mutane kimanin 100, da kuma dukiyoyin su na miliyoyin naira.

A cikin wata sanarwa Gwamnan Kebbi, Abubakar Bagudu ya fitar ta bakin mai magana da yawunsa, Abubakar Mu ‘azu Dakingari, ya ce gwamna ya ziyarci  yankin  Dolekaina don ganewa idonsa abinda ya faru, ya kuma taya su jaje da addu’ar Allah yak are faruwar hakan nan gaba.

Sanarwar ta kara da cewa gwamna ya umarci fitar da iyalan wadanda ambaliyar ruwan ta shafa, domin gudun kamuwa da cutaka. Har ila yau, ya ce za a kai su wani wuri mafi aminci da kuma tsabta, su samu abinci, ruwan sha, magungunan da kuma tsaro mai inganci.

Baya ga haka, Gwamna Bagudu tare da Marafan Dolekaina, Alhaji Muhammad Bello Suleiman, sun zagaya wurare da yawa da al’amarin ya shafa, inda suka ce a halin da ake ciki matsala ba iya Nijeriya kadai ta tsaya ba, har da kasar Nijar.

Har ila yau, Gwamna Bagudu ya ba da umurni a gudanar da kididdiga don a gano adadin mutanen ke gudun daga Arewa Maso Gabas, sakamakon rikicin Boko Haram, domin su ma a ba samu damar ci gaba da tallafa masu.

 

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

An Rantsar Da Sabbin Shugabanin Kungiyar Lauyoyi A Bauchi

Next Post

Yadda Aka Gudanar Da Bikin Dashen Shuka Itace A Jami’ar ABU Zariya

RelatedPosts

Babandede Ya Yi Gargadi A Kan Daukan Aiki Na Bogi Da Sunan NIS

Sauye-sauye Masu Ma’ana A Sashen Fasfo Na Hukumar Shige Da Ficen Nijeriya

by Yahuzajere
1 day ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), karkashin...

An Gabatar Da Huduba Kan Ramadan A Babban Masallacin Jos

An Gabatar Da Huduba Kan Ramadan A Babban Masallacin Jos

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Mohammed Ahmed Baba, Jos A ranar Juma'ar nan ne...

Yadda Tu’amalli Da Kayan Maye Ke Shafar Lafiyar Matasa Maza Da Mata  – Margaret

Yadda Tu’amalli Da Kayan Maye Ke Shafar Lafiyar Matasa Maza Da Mata  – Margaret

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Uwargida  Margaret  Juliu, sananniyar ce a jihar Kaduna,  musamman wajen fadakar...

Next Post

Yadda Aka Gudanar Da Bikin Dashen Shuka Itace A Jami’ar ABU Zariya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version