Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Makabarta A Gashuwa

by
11 months ago
in LABARAI
2 min read
Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Makabarta A Gashuwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Maitela,

Sakamakon ruwan sama mai karfi da aka yi kamar da bakin kwarya da safiyar ranar Litinin, ambaliyar ruwa ta mamaye wani bangaren babbar makabartar garin Gashuwa, shalkwatar karamar hukumar Bade a jihar Yobe.

Ruwan ya mamaye kimanin kaburbura 650 da ke cikin tsohuwar makabartar, wanda hakan ya jawo rushewar wasu da dama daga cikin wannan adadin, tare da faduwar bangaren katangar da ta zagaye wurin, wadda wajen yashi ne.

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

A zantawar sa da wakilinmu a jihar Yobe, shugaban karamar hukumar Bade, Alhaji Sanda Kara-Bade ya tabbatar da faruwar al’amarin tare da bayyana daukar matakan gaggawa wajen aiki da yan sa kai daga kungiyoyin agaji da sauran al’ummar gari don bayar da taimako don takaita barnar ruwan a makabartar.

“Haka kuma mun shaida wa gwamnatin jihar Yobe halin da ake ciki, wanda nan take ta dauki matakin gaggawa wajen tura kwararru domin daukar matakan kawo karshen malalar ruwa a makabartar.” in ji shugaban karamar hukumar Bade.

ADVERTISEMENT

Dangane da halin da ake ciki, Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe ya bai wa hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Yobe (SEMA) umurnin sake gina makabartar.

Shugaban hukumar (Edecutibe Secretary), Dr Mohammed Goje, shi ne ya bayyana haka ga manema labarai a Damaturu tare da sanar da cewa sun fara shirye-shirye, tattara kayan aiki da kwararru don fara aikin sake gina makabartar kamar yadda Gwamnan ya bayar da umurni.

“Mun fara shirye-shiryen aikewa da bulo da siminti tare da sauran kayan aiki don gyara makabartar cikin hanzari.”

A batu na daban kuma, wannan ba shi ne karon farko ba wanda ruwa ke mamaye makabartar tare da rusa makwantan, wanda hakan bai rasa nasaba da karancin magudanun ruwa a garin na Gashuwa, musamman wasu hanyoyin da aka gina ba tare da magudanun ruwa ba, kana da yadda jama’a ke ci gaba da gine- gine ba bisa ka’ida ba.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Lokaci Ya Yi Da ‘Yan Arewa Za Su Farka Kan Koma-bayan Yankin – Galadanci

Next Post

‘Yan Sanda Sun Ceto Dalibin Makarantar Bethel Da Wasu Mutum Biyu A Kaduna

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

by Leadership Hausa
5 hours ago
0

...

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

by Muhammad Bashir
7 hours ago
0

...

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

by Muhammad Bashir
16 hours ago
0

...

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

by
17 hours ago
0

...

Next Post
‘Yan Sanda Sun Ceto Dalibin Makarantar Bethel Da Wasu Mutum Biyu A Kaduna

'Yan Sanda Sun Ceto Dalibin Makarantar Bethel Da Wasu Mutum Biyu A Kaduna

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: