Amurka Ta Lalata Manufarta Ta Fadin Albarkacin Baki Wajen Watsa Labarai
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Lalata Manufarta Ta Fadin Albarkacin Baki Wajen Watsa Labarai

byCGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Tsohon wakilin kamfanin dillancin labaru na Anadolu na kasar Turkiya a birnin Beijing na kasar Sin Kamil Erdogdu ya rubuta wani sharhi mai taken “Amurka ta lalata manufarta ta fadin albarkacin baki wajen watsa labarai a wannan karo” a kwanakin baya.

Sharhin ya yi nuni da cewa, a ‘yan shekarun baya-bayan nan, kasar Sin ta kara daukar matakai wajen ba da labaran da ke faruwa a kasarta, tare da bude kofarta na maraba da abokai daga ko’ina a duniya don su kawo ziyara kasar. Amma kasar Amurka ta kashe kudade da dama a cikin shekaru 5 da suka wuce don horar da ‘yan jaridan kasashen yammacin duniya da su rika yada jita-jitar dake shafar kasar Sin. Wani masanin Turai Jan Oberg ya bayyana a kwanakin baya cewa, majalisar dokokin kasar Amurka ta zartas da wani daftarin doka a shekaru 5 da suka wuce, wanda ya shafi kashe kudi dala biliyan 1.5 don horar da ‘yan jarida da manyan editoci na kasashen yammacin duniya su rika rubuta labarai marasa kyau game da kasar Sin. Manufarsu ita ce yada jita-jita don hana bunkasuwar kasar Sin.

Sharhin ya ce, kasar Amurka ta yi hakan don kawo wa gwamnatinta moriyar tattalin arziki da siyasa. Bayan rushewar tarayyar Soviet, kasar Amurka tana bukatar kirkiro wata sabuwar abokiyar gaba. Bayan da kasar Sin ta kasance kasa ta biyu mafi bunkasuwar tattalin arziki a duniya, kasar Amurka ta mai da kasar Sin a matsayin abokiyar gaba.

Sharhin ya kara da cewa, ‘yan siyasar Washington na kasar Amurka sun kashe kudi fiye da dala biliyan daya don horar da ‘yan jaridan kasashen yammacin duniya yadda za su rika sabawa ka’idojin watsa labarai da yada jita-jita. Wannan batu ya lalata tsarin aikin ‘yan jarida da zubar da kimar jama’ar kasashen yammacin duniya, hakan ba zai zubar da mutuncin Sin a duniya ba, sai ma ya zubar da mutuncin gwamnatin kasar Amurka da na kafofin watsa labarun kasar. (Zainab Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
trump

Trump Ya Daukaka Kara Kan Hukuncin Hana Shi Shiga Zabe

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version