Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home KASASHEN WAJE

Amurka Za Ta Dandana Kudarta —Koriya Ta Arewa

by Tayo Adelaja
September 13, 2017
in KASASHEN WAJE
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Koriya ta Arewa, ta ce Amurka za ta dandana kudarta, sakamakon jagorantar zartar da matakin kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya, na kakaba mata sabbin takunkuman karya tattalin arziki.

Zalika manyan ami’an Koriya ta Arewan sun ce a kowane lokaci suna iya sake gwajin wani makamin Nukilyar, bayan nasarar da suka samu dari-bisa-dari a gwajin da suka yi a ranar 3 ga Satumba na makamin nukiliyar mai dauke da sinadarin Hydrogen.

Amurka na son kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya ya haramta wa cinikayyar danyen mai da Koriya ta Arewa, da kuma sanya wa shugaban Korea ta Arewan Kim Jong Un takunkumin tafiye-tafiye.

A farkon makon da muke, shugaba Kim Jong-Un ya gudanar da wani gagarumin bikin cin abinci domin karrrama masana kimiyar kasar, wadanda suka taimaka wa kasar kera makamin nukiliyar da aka gwada makon jiya.

Kamfanin dillancin labaran kasar ya ce shugaban ya gudanar da bikin ne tare da manyan hafsoshin sojin kasar, inda aka yi raye-raye da daukar hoto tare da shugaban.

Hotan da aka nuna na bikin na dauke da shugaba Jong-Un tare da wasu masana kimiyar kasar guda biyu Ri Hong Sop, na Cibiyar kera nukiliyar kasar da kuma Hong Sung Mu, mataimakin Daraktan Jam’iyyar da ke mulkin kasar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Tsarin Mulkin Togo: ‘Yan Adawa Sun Jajirce

Next Post

Gobe Za A Fara Sayar Da Tikitin Kallon Wasan Kwallon Kafa Na Duniya

RelatedPosts

Mijin Sarauniya Elizabeth Ta Ingila Ya Mutu

Mijin Sarauniya Elizabeth Ta Ingila Ya Mutu

by Muhammad
4 days ago
0

Rahotanni daga Fadar Buckingham ta kasar Ingila sun tabbatar da...

Nijer

Matan Nijer Sun Dage Kan ‘Yancinsu Bayan Kotu Ta Sako Wasu Shugabanninsu

by Muhammad
3 weeks ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Hukumomi a jamhuriyar Nijer sun sako...

Magufuli

Muhimman Abubuwa Goma Game Da Tsohon Shugaban Tanzaniya John Magufuli

by Muhammad
3 weeks ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Al'ummar kasar Tanzania suna zaman makokin...

Next Post

Gobe Za A Fara Sayar Da Tikitin Kallon Wasan Kwallon Kafa Na Duniya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version