Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home JAKAR MAGORI

An Azabtar Da Ma’aikacin Gidan Gona Da Garwashi Kan Satar Kwai Hudu

by Muhammad
March 18, 2021
in JAKAR MAGORI
1 min read
An Azabtar Da Ma’aikacin Gidan Gona Da Garwashi Kan Satar Kwai Hudu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabiu Ali Indabawa,

Wani ma’aikacin gidan gona mai suna Paulo, an ruwaito ya samu raunuka bayan da aka azabtar da shi da gawayi mai zafi saboda satar kwai hudu a kasar Zimbabwe. A cewar rahoton iHarare, wani mai suna Leon Koza ya kona kafafun dan shekara 34 mai suna Personal Paulo da garwashin wuta mai zafi, wanda a sanadiyyar hakan ya samu munananraunuka, inda rahotanni suka tabbatar da cewa shi surukin mai gonar Plumstead Farm ne inda yake aiki a ciki.

Da yake bayanin yadda lamarin ya faru, ma’aikacin manomin, Paulo ya bayyana cewa Koza wanda ya gano cewa ya saci kwai ya daure shi da wani karfe, ya yi masa duka da sanda har sai da kafafunsa suka kumbura, daga baya ya dauki gawayi mai zafi ya fara kone masa kafafun yana mai fada masa cewa sata ba kyau.

Ma’aikacin gonar ya kuma bayyana cewa an kai masa harin ne a ranar 6 ga Fabrairu kuma ya nemi likita ne kawai a ranar 26 saboda Koza ya yi masa barazanar zai sa a kama shi tare da korarsa daga gonar.

An kuma gano cewa Paulo ya sami damar zuwa neman magani ne kawai bayan ‘yar uwarsa, wacce ta ziyarce shi, ta gano cewa dan uwan ​​nata yana da raunuka a kafafunsa wanda ke zub da jini kuma ya kasa tafiya.

An gabatar da rahoto a Ofishin ‘yan sanda na Banket wanda ya kai ga cafke Koza, wanda tun lokacin da ya bayyana a gaban kotu kuma aka ba da izinin tsare shi a kan beli kyauta zuwa ranar 19 ga Maris 2021.

SendShareTweetShare
Previous Post

Masana Sun Nuna Mafita Ga Yadda Bashin Nijeriya Ya Yi Kamari

Next Post

Rikicin Hijabi: Kiristoci Sun Rufe Kofofin Shiga Makaranta Bayan Gwamnati Ta Bada Umarnin Budewa

RelatedPosts

Wiwi

NDLEA Ta Cafke Masu Fataucin Mutane Da Kwayoyi Na Naira Miliyan 564 A Abuja

by Muhammad
2 weeks ago
0

Babafemi ya ce wanda ake zargin mai shekaru 40 da...

kama

Yadda Danuwana Ya Tilasta Min Aikata Miyagun Laifuka –Wanda Ake Zargi

by Muhammad
2 weeks ago
0

A ranar Litinin Rundunar yan sandan karkashin jagorancin DCP Abbaa...

An Haifi Wani Yaro Da Azzakari Uku A Irak

An Haifi Wani Yaro Da Azzakari Uku A Irak

by Muhammad
2 weeks ago
0

Likitoci a Iraki sun bayar da rahoton haihuwar wani jariri...

Next Post
An Ci Gaba Da Ta’ziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamnan Kwara, AGF Abdul-Razak

Rikicin Hijabi: Kiristoci Sun Rufe Kofofin Shiga Makaranta Bayan Gwamnati Ta Bada Umarnin Budewa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version