Sagir Abubakar">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

An Bullo Da Shirin Noman IFAD Ne Don Zamanantarwa – Musa Malumfashi

by Sagir Abubakar
December 21, 2020
in RAHOTANNI
1 min read
Musa Malumfashi

PIC.1. FARMERS WORKING ON A RICE FARM IN ZUMBA, NIGER STATE ON SUNDAY (11/9/11).

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban shirin IFAD na Jihar Katsina, Alhaji Musa Hassan Malumfashi, ya ce, tsarin makarantar manoma ta zamani da a ka bullo da shi ya na daya daga cikin ingantattun hanyoyin ilimantar da manoma dabarun noma a zamanance.

Musa Malumfashi ya furta hakan ne a wajen shirin bayar da horo na kwana daya wanda aka shirya ma shugabannin shirin IFAD na kananan hukumomi da sauran ma’aikatan hukumar ta IFAD.

samndaads

Ya ce, daidai lokacin da a tsarin makarantu da ake zama aji domin koyar da dalibai, yake kasancewa a haka, shi wannan tsarin ana koyar da manoman ne dabarun noman cikin gonakin su.

Shugaban shirin IFAD dinna jihar Katsina ya shawarci masu samun horon dasu maida hankali kan abinda ake koyar dasu domin kuwa ana sa ran suma su koyar da sauran manoma a kananan hukumomi.

Shi ma da ya ke gabatar da kasida Dr. Gambo Muhammad ya ja hankalin masu daukar horon da su sa lura akan abinda ake koya mu su.

Haka kuma, a yayin da ya ke gabatar da ta shi makalar Alhaji Umar Lawal Mashi yayi bayanin alakar canjin yanayi da wannan tsarin da aka bullo dashi.

A daya bangaren kuwa, Alhaji Muhammad Zubairu Ganuwa ya koyar da mahalartan yadda za a magance matsalar zaizayar kasa da sauran makamantan matsaloli.

Kazalika, Alhaji Kabir Garba Hamisu da Alhaji Kabir Dodo, sun koyar da masu daukar horon yadda za su hada takin gargajiya.

Alhaji Kabir ya nuna masu karara yadda ake yi, ya kuma bukace su da su koyar da ‘yan uwansu manoma na gida.

SendShareTweetShare
Previous Post

Shehu Muhammadu Goma-goma Ya Yi Kira Ga Fulani Su Zama Tsintsiya Daya

Next Post

Masu Garkuwa Sun Nemi Diyyar Miliyan N25 Kan Tsohon Shugaban Karamar Hukuma A Kogi

RelatedPosts

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Sagir Abubakar
10 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Harkokin Noma

Sarkin Noma Ya Shawarci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Kokari Wajen Gyara Harkokin Noma

by Sagir Abubakar
11 hours ago
0

Daga Bala Kukkuru, Sarkin Noman Jihar Kano, Alhaji Yusuf Umar...

Kwazon Tambuwal

Hobbasar Kwazon Tambuwal Na Fara Biyan Albashi Daga Haraji A 2023

by Sagir Abubakar
1 day ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Gwamnatin Jihar Sakkwato a karkashin jagorancin...

Next Post
Shugaban Karamar Hukuma

Masu Garkuwa Sun Nemi Diyyar Miliyan N25 Kan Tsohon Shugaban Karamar Hukuma A Kogi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version