Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

An Cafke Hakimi Da Mutum 10 Bisa Fashi Da Makami A Neja

by Muhammad
December 28, 2020
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Tayil
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya,

Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta kame wani Hakimin Kauyen Tundan-Iliya da wasu mutum 10 bisa zargin kasancewa ‘yan fashi da makami a karamar hukumar Mashegu da ke jihar.
Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar ASP Wasiu Abiodun, ya shaida ta cikin sanarwar da ya fitar a jiya Lahadi a garin Minna, cewa biyo bayan rahoton sirri da ta sashin kwararru da suka samu a ranar 25 ga Disamba, tawagar ‘yan sanda ya kaddamar da samame zuwa maboyan ‘yan bindiga da ‘yan fashi da makami a dajin Tunga-Iliya.
Ya ce: “Tawagar ‘yan sandan sun nufi inda suke zargin ‘yan bindigan na boye inda suka yi musayar wuta, tare da kame mutum sha daya, daga cikinsu mutum biyar sun gamu da raunuka.
“Daga cikin wadanda aka kama bisa zargin fashi da makamin har da Sarkin kauyen Tunga-Iliya da wata mai suna Summaya Bello wacce take nemo bayanai tare da sanar da ‘yan fashin bayanai,” inji shi.
Abiodun, ya kuma kara da cewa ‘yan sanda tunin sun fara zurfafa bincikensu kan lamarin kana da zarar suka kammala za su gurfanar da wadanda suka kama din a gaban kotu domin fuskantar tuhuma daidai da laifukansu.
Ya kara da cewa a ranar 25 ga watan Disamban 2020 sun samu rahoton cewa wasu ‘yan bindiga sun mamaye unguwan Gambo da ke karamar hukumar Rafi inda su ka yi garkuwa da mutum hudu.
Ya shaida cewar an samu ceto mutum daya yayin da a ke cigaba da kokarin ceto sauran.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Ministar Mata, Pauline Tallen, Ta Kamu Da Cutar Korona

Next Post

Zanga-zangar EndSARS Ta Tabbatar Da Kasancewarmu Masu Son Zaman Lafiya –Sheikh Yahaya  

RelatedPosts

IPOB

IPOB Ta Bayyana Dalilin Arangamarta Da Sojoji

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

A jiya ne 'Yan asalin Biafra (IPOB) da aka haramta...

NDLEA Ta Damke Mutum 544 Bisa Zargin Fataucin Kwayoyi A Borno

NDLEA Ta Damke Mutum 544 Bisa Zargin Fataucin Kwayoyi A Borno

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Shugaban hukumar yaki da sha tare da fataucin miyagun kwayoyi...

‘Yan Sanda Sun Ceto Yara Takwas, Sun Kama Masu Juna-biyu A Anambara

‘Yan Sanda Sun Ceto Yara Takwas, Sun Kama Masu Juna-biyu A Anambara

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

An kama wasu mata takwas, ciki har da mata masu...

Next Post
Zaman Lafiya

Zanga-zangar EndSARS Ta Tabbatar Da Kasancewarmu Masu Son Zaman Lafiya –Sheikh Yahaya  

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version