Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutum Hudu Da Kokon Kai A Jihar Ogun

by
3 years ago
in Tauraruwa Mai Wutsiya
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Waiwayen Kanun Labarai Daga Litinin 15 Zuwa 18 Ga Sha’aban 1442 Bayan Hijira

’Yan Sanda Sun Gabatar Da Masu Manyan Laifuka 17 A Jos

Rundunar ‘yan sandar jihar Ogun ta cafke wani boka mai suna Jamiu Olasheu dan shekara 35 tare da wasu mutum uku, bisa samun su da kokon kai. An bayyana cewa ‘yan sanda da ke gudanar da aiki a yankin Agbara su ne suka cafke mutum biyu wadanda suke kan babur a Kofedoti cikin garin Agbara. Lokacin da aka caje mutanen Teslim Ayeniromo dan shekara 45 da kuma Sunday Kolade mai shekaru 35, sai aka samu kokon kan a cikin buhu.
Da yake tabbatar da kamen, kakakin rundunar ‘yan sandar jihar Abimbola Oyeyemi ya bayyana cewa, nan take aka cafke mutum biyun sannan aka garzaya da su zuwa shalkwatar ofishin ‘yan sanda da ke Agbara, inda DPO Adegbite Omotayo yake gudanar da binciken lamarin.
Oyeyemi ya kara da cewa, bisa bincike da aka gabatar ya nuna cewa, wadanda ake zargin sun yi ikirarin cewa wani mutum mai suna Michael Osanyinbi dan shekara 51, shi ne ya ba su wannan kokan kan domin su kai wa boka. Wadanda ake zargin sun jagoranci DPO zuwa gidan mutumin tare da bokan wanda za a bai wa kokon kan, ‘yan sanda sun cafke dukkanin su. Oyeyemi ya ce, “Bokan ya yi bayani inda yake cewa shi ne ya bukaci wannan kokon kai, Michael Osanyinbi ya yi alkawarin zai ba da naira 25,000 tare naira 1,000 kudin babar ga wadanda za su samo wannan kokon kai. Ya kara da cewa, ya bukaci wannan kokon kai ne domin a yi tsafi da shi.
A halin yanzu dai, kwamishinan ‘yan sandar jihar Ahmed Iliyasu ya bayar da umurnin a yi gaggawar mika wadanda ake zargi zuwa sashin rundunar ‘yan sanda masu binciken manyan laifuka domin gudanar da cikakken bincike tare da gurfanar da su a gaban shari’a.”

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

‘Yan Sanda Na Neman Mutumin Da Ya Kashe Wata Mata A Legas

Next Post

Ma’aikaciyar Banki Ta Shiga Hannu Bisa Laifin Damfarar Dangote

Labarai Masu Nasaba

Labarai

Waiwayen Kanun Labarai Daga Litinin 15 Zuwa 18 Ga Sha’aban 1442 Bayan Hijira

by
1 year ago
0

...

’Yan Sanda Sun Gabatar Da Masu Manyan Laifuka 17 A Jos

by
3 years ago
0

...

Wata Mata Ta Kwace Jariri Daga Hannun Mahaifiyarsa A Ekiti

by
3 years ago
0

...

Benin: Wani Mutum Ya Kashe Surukansa Uku Saboda Tsananin Zalunci

by
3 years ago
0

...

Next Post
Ma’aikaciyar Banki Ta Shiga Hannu Bisa Laifin Damfarar Dangote

Ma’aikaciyar Banki Ta Shiga Hannu Bisa Laifin Damfarar Dangote

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: