Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

An Ci Tarar Kano Pillars Miliyan 9 Da Kwace Mata Maki Uku

by Abba Ibrahim Wada
3 weeks ago
in WASANNI
1 min read
Kano Pillars
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Hukumar dake kula da gudanar da gasar Firimiyar Nijeriya ta ci tarar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars naira miliyan tara, bayan da ta sameta da laifin karya dokar gasar haka kuma hukumar ta kwashe maki uku daga wanda Pillars take da shi, duk dai a cikin hukuncin da aka yanke mata.

Wannan hukuncin ya biyo bayan da magoya bayan Kano Pillars suka ragargaji motar Katsina United, bayan wasan hamayya da Katsina United karawar mako na 22 ranar Lahadi a filin wasa na Sani Abacha da ke Jihar Kano. Wannan kuma shi ne karon farko da Kano Pillars ta yi fafatawa a gida, tun bayan kakar wasa biyu da take buga wasanninta a Jihar Kaduna, bayan da filin wasa na Sani Abacha bai cika ka’idar karbar bakuncin wasannin Firimiyar Nijeriya ba.

  • Kano Pillars Ta Koma Ta Hudu A Firimiyar Nigeriya

Kawo yanzu Pillars za ta biya tarar Naira miliyan tara, an kuma kwashe mata maki uku, za ta koma buga wasannin da suka rage mata a filin wasa na MKO Abiola da ke Babban Birnin Tarayya Abuja. Haka kuma za a sake cire mata maki uku nan gaba idan an sake samun kungiyar da tayar da hatsaniya kuma cikin hukuncin an umarci Kano Pillars da ta gyara motar Katsina United da aka lalata a lokacin da za ta karkare wasanninta a Abuja.

Labarai Masu Nasaba

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

Da wannan maki ukun da aka kwashe, Kano Pillars ta yi kasan teburi zuwa ta 16 da tazarar maki biyu tsakaninta da ‘yan karshen teburi sannan Pillars din za ta buga wasan mako na biyun da ba a karasa shi ba da Katsina United a Abuja ranar Litinin mai din nan.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

Next Post

Yadda Ake Ittikafi Da Kuma Hukunce-Hukuncensa

Labarai Masu Nasaba

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
3 days ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
3 days ago
0

...

barcelona

Barcelona Ta Sa Hukumar La Liga Asarar Makudan Kudade

by Abba Ibrahim Wada
3 days ago
0

...

Nijeriya Ta Dakatar Da Shiga Wasannin Kwallon Kwando Tsawon Shekara Biyu

Nijeriya Ta Dakatar Da Shiga Wasannin Kwallon Kwando Tsawon Shekara Biyu

by Abba Ibrahim Wada
4 days ago
0

...

Next Post
Yadda Ake Ittikafi Da Kuma Hukunce-Hukuncensa

Yadda Ake Ittikafi Da Kuma Hukunce-Hukuncensa

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: