Rabiu Ali Indabawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASASHEN WAJE

An Cika Watanni 6 Da Fara Fuskantar Annobar COBID-19 A Duniya

by Rabiu Ali Indabawa
July 1, 2020
in KASASHEN WAJE
2 min read
Gujewa Cutar Covid-19 Shugaban Karamar Hukumar Lafia Ya Kaddamar Da Sabon Garejin Mota
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daidai lokacin da ake cika watanni 6 da bullar cutar coronabirus ko kuma COBID-19 a duniya, hukumar lafiya ta WHO ta yi gargadin cewa ko kadan ba a wuce annobar cutar coronabirus ba, domin kuwa a yanzu haka somin tabi aka fara gani na bannar da cutar za ta yiwa duniya.

Cikin bayanan da WHO ta fitar jiya, bayan cika watanni 6 da bullar cutar wadda a karon farko ta bayyana a yankin Wuhan na tsakiyar China, shugaban hukumar Tedros Adhanom, ya ce duk da matakan da kasashen duniya ke dauka na yaki da cutar a kowacce rana adadin masu kamuwa da ma wadanda ke mutuwa na sake karuwa, wanda ke nuna bannar da cutar za ta tafkawa duniya gabanin zuwa karshenta.

samndaads

Tedros Adhanom a jawabin nasa, ya ce watanni 6 da suka gabata, babu wanda ya yi tunanin annobar cutar ta coronabirus da ta faro daga China za ta jefa duniya a halin tsaka mai wuya.

Acewar hukumar ta WHO yaki da coronabirus na bukatar hakuri tare da aiki tare, domin kuwa sai an hada hannu ne za a iya yaki da ita, yana mai cewa sai a nan gaba ne cutar za ta kai ganiyarta.

Bugu da kari, Majalisar Dinkin Duniya ta ce annobar coronabirus ta jefa akalla yara sama da miliyan 100 a yankin Kudancin Asia cikin talauci sakamakon yadda cutar ta shafi tattalin arzikin yankin. Daraktan Hukumar da ke kula da Yankin Jean Gough ya ce matsalar ta shafi yin rigakafin cuttutuka da samar da abinci mai gina jiki da kayan more rayuwa, inda ya bukaci daukar matakan gaggawa domin rage radadin matsalar.

Yankin kudancin Asia na dauke da yara miliyan 600 da suka fito daga kasashen India da Pakistan da Afghanistan da Nepal da Bangladesh da Sri Lanka da Maldibes da Bhutan, kuma miliyan 240 daga cikin su na fama da tsananin talauci.

A wani rahoton kuma, karuwar adadin masu dauke da cutar coronabirus a sassan duniya ta sa hukumomi a wasu kasashe, ciki har da India da Amurka, sun sake kakaba dokokin kulle, yayin da shugaban hukumar lafiya ta duniya WHO ya ce har yanzu ba a dauki hanyar shawo kan cutar ba.

India ta ba da rahoton samun karin adadi mafi yawa na wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar a jiya Litinin inda ta samu mutum 20,000, wanda ya haura sama da dubu mutum 100,000 da aka gani a cikin mako daya.

Kasar ita ke biye da Amurka, Brazil da kuma Rasha a adadin wadanda aka tabbatar sun harbu tun lokacin da annobar da ta faro daga China a karshen shekarar da ta gabata.

Sai dai wani bangare na jihar Assam da ke Indiar ya sake kakaba dokar kulle har zuwa 12 ga watan Yuli, yayin da jihar West Bengal ta kara tsawaita dokokin kullenta har zuwa karshen watan na Yuli.

A Amurka kuwa, jihohin Tedas, Florida, Arizona da kuma California na daga cikin wadanda suka ga karin wadanda suka kamu da cutar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Dan Wasan Nijeriya Ya Lashe Kyautar Gwarzon Gidan Radio Faransa

Next Post

Macron Zai Halarci Taron Kasashen Sahel A Mauritania

RelatedPosts

Amurkawa

Biden Ya Gabatar Da Shirinsa Na Yi Wa Dukkan Amurkawa Rigakafi

by Rabiu Ali Indabawa
2 days ago
0

Zababben shugaban Amurka Joe Biden ya gabatarwa Amurkawa shirinsa na...

Jamhuriyar Afrika

Yawan ‘Yan Jamhuriyar Afrika Ta Tsakiya Da Ke Gudun Hijira Ya Ninka Cikin Mako Daya

by Rabiu Ali Indabawa
2 days ago
0

Majalisar Dinkin Duniya ta ce adadin ‘yan gudun hijirar dake...

Masu Neman Mafaka Sun Fara Tattaki Daga Honduras Zuwa Amurka

by Rabiu Ali Indabawa
3 days ago
0

Wani sabon ayarin dubunnan masu neman mafaka a Honduras sun...

Next Post
An Cika Watanni 6 Da Fara Fuskantar Annobar COBID-19 A Duniya

Macron Zai Halarci Taron Kasashen Sahel A Mauritania

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version