Abba Ibrahim Wada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

An Dage Babban Zaben Shugaban Barcelona

by Abba Ibrahim Wada
January 18, 2021
in WASANNI
2 min read
Zaben Shugaban Barcelona
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta bayar da sanarwar cewa tad age babban zaben shugaban kungiyar wanda aka tsara za’ayi a yau sakamakon dalilan cutar Korona da kuma shawarar da hukumomin kasar suka bayar.

Da farko dai an tsara cewa za’a gudanar da zaben ne a ranar 19 ga watan Janairu domin zabeb shugaban kungiyar saboda a halin yanzu kungiyar tana hannun rikon kwarya sai dai dalilai sun sanya an sake dage zaben.

Manyan ‘yan takarkaru dai da dama sun shirya fafatawa a zaben wanda yake cike da kalubale musamman ga wanda ya samu nasara domin akwai matsaloli jingim a kungiyar wadanda suke bukatar kallo na gaggawa.

Tsohon shugaban kungiyar, Joan Laporta ne a kan gaba tsakanin ‘yan takarar dake neman darewa shugabancin kungiyar bayan rage ‘yan takarar zuwa 4 daga 9 da akayi a kwanakin baya saboda magance sabon rikici bayan zabe.

Mai bi masa kuwa shine Bictor Font wanda yake da goyon bayan mutane dubu 4 da dari 710, tsohon jami’in hukumar gudanarwar Barcelona Toni Freida ya samu sa hannn mutane dubu 2 da dari 821, sai kuma tsohon mataimakin shugaban kungiyar Emili Rousaud da ya samu dubu 2 da dari 510.

Da farko dai babu sunan Laporta a cikin jerin ‘yan wadanda ake saran zasu fafata a babban zaben da za’ayi a wannan kakar sai dai tuni hankali ya koma kansa inda ake ganin zai iya sake komawa shugabancin kungiyar a karo na biyu.

Duk da cewa har yanzu babu wanda zai fayyace irin manufofin Laporta musamman dan gane da makomar dan wasan kungiyar kuma kaftin, Leonel Messi da kuma halin da kungiyar ta shiga na rashin kudi sakamakon annobar cutar Korona.

Har yanzu dai ba a sake bayyana ranar da za’ayi wannan zabe ba amma wasu rahotanni sun tabbatar da cewa a cikin watan Fabrairu mai zuwa za a yi zaben wanda shine karo na farko tun bayan sauka daga mukamin shugabancin kungiyar Jose Maria Bartemeu ya yi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Rikita-Rikitar Da Ta Baibaye Dangantakar Ozil Da Arsenal

Next Post

Wace Kungiya Ce  Zata Dauki Diego Costa

RelatedPosts

Atletico

Za A Yi Kare Jini Biri Jini Tsakanin Real Madrid Da Atletico Gobe

by Abba Ibrahim Wada
9 hours ago
0

A ranar Lahadi ne Real Madrid za ta ziyarci filin...

Bale

Real Madrid Ce Kawai Zata Fayyace Makomar Gareth Bale -Mourinho

by Abba Ibrahim Wada
9 hours ago
0

Kocin kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Jose Mouinho ya ce,...

Sevilla

Daman Nasan Muna Da Nasara A Kan Sevilla -Messi

by Abba Ibrahim Wada
9 hours ago
0

Dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Barcelona, Leonel Messi, ya...

Next Post
Diego Costa

Wace Kungiya Ce  Zata Dauki Diego Costa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version