An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

byAbubakar Sulaiman
3 months ago
Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar wasu ɗalibai biyu na Makarantar Kwalejin Sakandare ta Gwamnati da ke Bichi, biyo bayan wani hari da wasu ɗalibai suka kai musu a cikin harabar makarantar.

Ɗaliban da suka rasu, Hamza Idris Tofawa da Umar Yusuf Dungurawa, an ce an kai musu hari da wani abu mai kaifi da ake kira ‘Gwale-Gwale’, wanda wasu tsofaffin ɗalibai suka yi amfani da shi bayan da suka zargesu da aikata wani laifi da ba a bayyana ba, kuma suka ɗauki doka a hannunsu.

  • VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Wayar da Kan Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, ya fitar ranar Talata, 16 ga Yuli, 2025.

Sanarwar ta ce Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dr. Ali Haruna Makoɗa, ta bakin Babban Sakataren Ma’aikatar, Alhaji Bashir Baffa Muhammad, ya bayar da umarnin gudanar da bincike na gaskiya da adalci don gano haƙiƙanin abin da ya faru.

Babban Sakataren wanda ya kai ziyara makarantar, ya shawarci ɗalibai da su guji ɗaukar doka a hannunsu. “Ya kamata ku riƙa kai korafe-korafenku ga hukumomin makaranta domin ɗaukar matakin da ya dace,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan da lamarin ya rutsa da su, tare da addu’ar Allah ya ba wa marigayyu Aljannatul Firdaus.”

Ƙin jin daɗin iyalan ya fito fili, inda Malam Ibrahim Yusuf Dungurawa, dangin marigayi Umar, ya bayyana yadda suka firgita da jin labarin mutuwar ɗansu, yana mai roƙon gwamnati da ta tabbatar da adalci. Haka zalika, Malam Idris Garba Tofawa, mahaifin marigayi Hamza, ya bayyana lamarin a matsayin ƙaddara daga Allah, amma ya bukaci hukuma ta ɗauki mataki cikin gaggawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version