Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

An Fi Samun Koma-bayan Kasuwancin Hatsi A Bana – Alhaji Magaji

by
6 months ago
in NOMA
2 min read
An Fi Samun Koma-bayan Kasuwancin Hatsi A Bana – Alhaji Magaji
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Awwal Umar, Minna

 

Shugaban kungiyar masu awon hatsi na Jihar Neja, Alhaji Magaji Umaru ya bukaci gwamnati ta kara kaimi wajen samar da tsaro ta yadda manoma za su samu saukin wajen gudanar da harkokin noma.

Labarai Masu Nasaba

Sharhi: Rashin Karfafa Noman Auduga Tamkar Kamun Gafiyar Baidu Ne Ga Nijeriya

Noman Rogo: Yadda Nijeriya Ke Asarar Naira Tiriliyan 27 A Kasuwar Duniya

Shugaban ya yi kiran ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Minna farkon makon nan.

 

Shugaban ya ce kasuwancin hatsi a wannan shekarar an fi samun koma-baya musamman yadda mahara suka mamaye dazuka tare da hana wa manoma damar kusantar amfanin gonakinsu, wanda hakan ke kokarin tilasta tsadar abinci a jihar. Ya ci gaba da cewar duk da barazanar karancin ruwan sama da aka samu a damanar bana, manoma da suka samu damar tabukawa kuma na fuskantar kalubalen mahara wanda hakan ke tilasta abincin da aka samu yake kokarin lalacewa a gonaki ba rare da an kawo shi gida ba.

 

Ya ce wuraren da ake samun damar shiga dan sawo abinci ba hanya, wanda bisa tilas suke hakura da dan abin da ke shigowa, shi ya sa farashin abinci ya kasa saukowa duk da cewar an shiga kakar amfanin gona.

 

Da ya juya kan zargin da ake yi wa ‘yan kasuwar na boye abinci kuwa, ya ce ai ba dan kasuwar da zai so ware kudade dan juyawa ya yi tunanin sayen abinci ya boye dan tunanin ya yi tsada sannan ya sayar, dukkan kayan da ka gani nan rashin ciniki ne da tsadarsu ya sa ka gan shi a jibge haka.

 

“Dan haka, ina jawo hankalin gwamnati ganin tana da kudurin bunkasa bangaren noma ta taimaka wa manoma da kayan aiki kan kari ta yadda za su samu damar yin noman rani.

 

“Jihar nan Allah ya albarkace ta da kasar noma wanda kuma idan za a taimaka lallai za a iya noma sau uku a shekara, hakan ne zai saukaka tsadar farashin abinci,” in ji shi.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Community Policing: Mafita Ga Matsalolin ‘Yan Sanda!

Next Post

Wasu Fitattu Da Ranakun Haihuwarsu A Makon Nan

Labarai Masu Nasaba

Sharhi: Rashin Karfafa Noman Auduga Tamkar Kamun Gafiyar Baidu Ne Ga Nijeriya

Sharhi: Rashin Karfafa Noman Auduga Tamkar Kamun Gafiyar Baidu Ne Ga Nijeriya

by Abubakar Abba
2 weeks ago
0

...

Rogo

Noman Rogo: Yadda Nijeriya Ke Asarar Naira Tiriliyan 27 A Kasuwar Duniya

by Abubakar Abba
3 weeks ago
0

...

Gurjiya

Sirrin Noman Gurjiya Wajen Bunkasa Tattalin Arziki

by Abubakar Abba
4 weeks ago
0

...

Bunsuru

Kiwon Bunsuru A Saukake

by Abubakar Abba
1 month ago
0

...

Next Post
Gwamnan Bauchi

Wasu Fitattu Da Ranakun Haihuwarsu A Makon Nan

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: