Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Gudanar Da Addu’ar Bakwan Editan Labaran LEADERSHIP A YAU, Umar Hunkuyi

by Muhammad
December 24, 2020
in LABARAI
1 min read
Hunkuyi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Bello Hamza

 

samndaads

A jiya Laraba ne al’umma da dama su ka samu halartar addu’ar cika kwanaki bakwai da rasuwar Malam Umar Abubakar Chiroma Hunkuyi, Editan Labarai na LEADERSHIP A YAU.

An dai gudanar da addu’ar ne a kofar gidansa da ke Layin Abuja a unguwar Rigasa da ke garin Kaduna da kuma Layin Mangwarori da ke Hayin Dogo Samaru a Zariya duka a lokaci daya.

A cikin jawabinsa bayan kammala addu’ar, Malam Ibrahim Musa ya yi kira ga zuriyar da marigayin ya bari da su hada kansu, su kuma tsayu a kan kyawawar tarbiyar da ya dora su a kai.

“Yakamata ku zama tsintsiya madaurinki daya. Ta haka za ku ci ribar zaman duniya ku kuma tsayuwa a kan kyawawar tarbiyar da ya dora ku a kai,” in ji shi.

A garin Samaru kuma tun da sanyin safiya ne dimbin jama’a su ka taru a kofar gidansu da ke Layin Mangwarori a Hayin Dogo, inda a ka gabatar da saukar Alkur’ani Mai Tsarki, inda daga nan ne Liman Umar Sambo da Malam Lukman Alfa su ka jagoranci sauran malamai wajen gabatar da addu’ar neman gafara da rahama ga ruhin Marigayi Malam Umar Chiroma.

Shi dai Malam Umar dan asalin garin Hunkuyi ne da ke karamar hukumar Kudan ta Jihar Kaduna; karatu da aikin gwamnati su ka kawo shi Samaru Zaria, daga baya kuma ya dawo garin Kaduna, inda Allah ya karbi rayuwarsa a ranar Laraba 16 ga Disamba, 2020.

Ya rasu ya bar mata daya da ’ya’ya 16. Allah ya gafarta ma sa. Amin.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Bada Hutun Kirsimeti Da Sabuwar Shekara

Next Post

Malaman Jami’a Sun Dakatar Da Yajin Aiki Bayan Wata Tara

RelatedPosts

Zaben Dan Majalisa

Za A yi Zaɓen Gwamnan Anambara Ranar 6 Ga Nuwamba – INEC

by Sulaiman Ibrahim
4 hours ago
0

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa a ranar...

Ogun

Fashewar Tankar Mai Ya Ci Rayuwar Mutum Uku Da Jittaka Shida A Ogun

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, A ranar Talata ne mutum uku...

Bafarawa

’Yan Nijeriya Sun Fi So A Magance Rashin Tsaro Fiye Da Korona, Cewar Bafarawa

by Muhammad
11 hours ago
0

A Juya Kuɗin Rigakafin Cutar Naira Biliyan 400 Zuwa Tsaro...

Next Post
Jami'a

Malaman Jami’a Sun Dakatar Da Yajin Aiki Bayan Wata Tara

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version