An Gurfanar Da Jami'an EFCC 2 Kan Zargin Kisan Abokin Aikinsu 
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Jami’an EFCC 2 Kan Zargin Kisan Abokin Aikinsu 

byCMG Hausa
2 years ago
EFCC

Hukumar Yaki da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC) ta ce, wani jami’inta mai suna Insifekta Abel Isah Dickson ya mutu bayan rashin jituwa da hatsaniya da ta shiga tsakaninsu da wasu abokan aikinsa guda biyu kan wasu kayayyakin da aka amso daga wajen wani da ake zargi a Jihar Sokoto. 

 

Kakakin hukumar ta EFCC, Wilson Uwujaren, ya ce, kayayyakin sun hada da magunguna da wasu kudade.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Lasisin Bude Jami’ar Koyo Daga Gida Da Karin Wasu 37

EFCC ta bayyana sunayen jami’an biyu sun hada da Mataimakin Sufuritendan hukumar EFCC, Apata Oluwaseun Odunayo da Insifekta na hukumar EFCC, Ogbuji Titu Tochukwu, wadanda tunin aka cafke su tare da gurfanar da su a kotu a jihar Sokoto kan zargin kisan kai.

 

Uwujaren ya kuma ce, shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa, za su tabbatar an wanzar da adalci wajen hukunta jami’an, ya ce, an dakatar da jami’an biyu yayin da bincike ke cigaba da gudana.

 

Ya ce, Bawa ya sha alwashin ba zai lamunci wani dabi’a ta rashin da’a ba, “Shugabanmu, Abdulrasheed Bawa, ya kadu da wannan lamarin kuma ya jajantawa iyalan jami’in da ya rasa ransa.

 

“Ya kuma tabbatar da cewa jami’an da suka yi sanadiyyar rasa jami’in namu tabbas za su fuskanci hukunci har sai adalci ya wanzu.”

 

Kazalika, Bawa ya gargadi jami’ansa da su daina kokarin kauce wa ka’idar aiki da koyarwar da aka musu. Ya nuna cewa ba za su lamunci rashin bin matakan aiki da koyarwar da aka yi wa jami’an ba.

 

“A halin da ake ciki, an bisne jami’in namu da ya mutu a ranar Asabar 13 ga watan Mayun 2023 a Jos ta jihar Filato.”

 

“Matashin jami’in namu ya mutu ne a ranar 7 ga watan Mayun 2023 a asibitin koyarwa na jami’ar Usmanu DanFodiyo da ke Sokoto yayin da ke amsar kulawar Likitoci bayan raunukan da ya samu kwanaki biyu kafin nan a wani hatsaniyar da ya barke tsakaninsa da wasu jami’anmu biyu masu suna Apata Oluwaseun Odunayo da Insifekta Ogbuji Titu Tochukwu.

 

“Sun samu rashin jituwar ne kan wasu tsarin ajiye wasu kaya mallakin wani da ake zargi da ke tsare, hakan ya kai su ga yin fada, lamarin da hukumar nan ta yi tir da shi.

 

“Jami’an biyu an dakatar da su kuma an mikasu ga ‘yansandan Nijeriya inda suka gurfanar da su.

 

“An shigar da su kara ne kan zarge-zargen guda biyu da suka hada da hada baki wajen aikata kisan gilla a gaban babban Kotun Majistire, Gwiwa da ke Sokoto.”

 

“Laifukan biyun su na da hukunci a karkashin sashe na 60 da na 191 na dokar final kod ta Jihar Sokoto, 2019.

 

“Ba tare da nuna kyama ga binciken ‘yan sanda ba, za su kuma fuskanci karin matakan ladabtarwa bisa ka’idojin ma’aikatan hukumar.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
Next Post
Darajar Hajojin Da Masana’antun Sin Ke Sarrafawa Ta Karu Zuwa Kaso 5.6 Bisa Dari A Afirilu

Darajar Hajojin Da Masana’antun Sin Ke Sarrafawa Ta Karu Zuwa Kaso 5.6 Bisa Dari A Afirilu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version