An Gurfanar Da Wani Matashi A Gaban Kotu Kan Zargin Kashe Wata Mata Da 'Yarta A Kebbi
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Wani Matashi A Gaban Kotu Kan Zargin Kashe Wata Mata Da ‘Yarta A Kebbi

bySulaiman
3 years ago
Kebbi

An gurfanar da wani mutum mai suna Idris Suleiman a gaban wata babbar kotun jihar Kebbi, bisa laifin kashe wata matar aure da diyarta ‘yar shekara hudu a unguwar Kamfanin Labana da ke cikin Birnin Kebbi.

Wanda ake tuhuma dai Idris Suleiman dan asalin Jamhuriyar Nijar ne ke fuskantar tuhuma biyu na aikata laifin kisan kai da ake iya yanke hukuncin kisa a karkashin sashe na 191 (a) na dokar Penal Code na jihar Kebbi 2021.

  • Zargin Yada Luwadi: Saudiyya Ta Hana Sayar Da Kayan Wasa Na Yara Masu Siffanta Jinsin Mutum

Wakilinmu ya tuna cewa wanda ake zargin ya daba wa matar wuka ne har lahira sannan ya bugi kan karamar yarinyar a kan fale-falen dakin mahaifiyar wanda ya yi sanadin mutuwarta ita ma.

Da take gurfanar da wanda ake zargin a gaban mai shari’a Suleiman Ambursa kuma shi ne babban jojin jihar Kebbi, Darakta mai shigar da kara ta ma’aikatar shari’a a Jihar (DPP), Barista A’isha Abbas tare da Barista Zainab Jabbo da kuma Barista Aminu Diri sun shaida wa kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin ne watanin biyu zuwa na uku da suka gabata a cikin hurumin wannan kotun.

Domin tabbatar da aikata laifin , DPP ta kira shaidu shida tare da gabatar da shaidarsu a gaban kotun a karkashin mai shari’a Sulieman Muhammad Ambursa da ke kotu ta daya a Birnin Kebbi.

Bayan gabatar da shaidar shaidun, lauyoyin masu gabatar da kara sun rufe karar nasu.

Lauyoyin da ake kariyar Wanda ake tuhuma a cikin karar mai lamaba KB/HC/27C/2022, Barista Alhassan Salisu-Muhammad, wanda kuma shi ne Shugaban ofishin Lauyoyin masu kare marasa galihu a Jihar Kebbi tare da wasu lauyoyin da suka riga sun hada da; Barista Iliyasu Adamu da Mrs Afu M. A. suka bude nasu kariya kuma sun tabbatar wa da kotun cewa sun kammala ba da kariyar su a gaban kotun.

Haka kuma Lauyoyin da ke kare wadanda ake tuhuma sun kira shaida guda daya (wanda ake tuhuma) don tabbatar da kare su tare da rufe ba da kariyar su nan take.

Daga nan, Lauyoyin masu gabatar da kara da kuma masu kare wanda ake tuhuma sun nemi izinin kotun ta dage shari’ar zuwa ranar 30 ga watan Yuni, don gabatar da dukkan hujojin su da kuma yin mahawara kan hujojin a gaban kotun.

Alkalin kotun dai, ya dage sauraren karar zuwa ranar 30 ga watan Yuni domin amincewa da rubutaccen hujojin na lauyoyin bangare biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

Jami'an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version