An Hana 'Yan Jarida Shiga Wajen Tattara Sakamakon Zabe A Adamawa
  • English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Hana ‘Yan Jarida Shiga Wajen Tattara Sakamakon Zabe A Adamawa

byMuh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Adamawa

Jami’an tsaro sun hana ‘yan jarida shiga ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), inda ake tattara sakamakon zaben gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jiha da aka karasa a Jihar Adamawa.

Jami’an tsaron sun shaida wa manema labarai cewa “An ba mu umarni daga sama, cewa kada mu kyale kowane dan jarida ya shiga, sai wanda aka tantance, saboda haka ba za a bari kowa ya shiga ba.

  • Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
  • Peng Liyuan Ta Gana Da Uwargidan Shugaban Brazil

“Babu wani dan jarida da zai shiga sai wanda aka tantance, shi ne umarnin da aka ba mu daga sama” in ji jami’an ‘yan sandan.

Dama dai akwai bayanai da ke yawo a jihar cewa akwai wasu mutane da suke ganin ko za ayi kare-jini biri-jini sai sun cimma manufarsu ta siyasa a lokacin zaben.

Lamarin da ya sa kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar PDP a jihar, nuna damuwa kan cewa ba zai amince da duk wani matakin da zai yi kazalandan ga bayyana sakamakon zaben.

A kwanan baya ne wani sakon muryar kwamishinan hukumar zabe ta jihar Barista Hudu Yunusa Ari, yana ba da umrni ga baturen zabe na karamar hukumar Fufore, da ke cewa “A taimaki matanen nan” da ya ke ita ce kawai mace guda da ta tsaya zabe.

Daga baya hukumar zaben ta ayyana zaben da cewa bai kammala ba, duk da dan takarar jam’iyyar PDP, gwamna Ahamdu Umaru Fintiri, na kan gaba ga ‘yar takarar jam’iyyar APC, Aishatu Dahiru Ahmad Binani, da kuri’u sama da dubu 31.

Rahotanni dai na nuni da cewa INEC, za ta sauya wurin da ta ke tattara sakamakon zaben zuwa wani wajen da ba a kai ga tantancewa ba zuwa lokacin hada wannan rahoton.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Next Post
Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanonin Kasar Cikin Jerin Sunayen Kamfanonin Da Ta Sanya Musu Takunkumi

Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanonin Kasar Cikin Jerin Sunayen Kamfanonin Da Ta Sanya Musu Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025
Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

October 7, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version