An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna

byAbubakar Abba
2 years ago
Makiyaya

An shirya taron bita na kwana daya kan yadda fulani makiyaya za su rika shuka ciyawa a Jihar Kaduna, domin ciyar da shanu da sauran dabbobinsu tare kuma da bunkasa kasuwancinta (ciyawar), tuni dai aka ware musu kadadar da za su fara shuka wannan ciyawa.

Haka zalika, matan fulani makiyayan kuma za a ba su shanu domin su fara samar da wadatacciyar madara a fadin jihar da kuma kasa baki-daya.

  • Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa
  • Sabon Salon ‘Yan Bindiga Na Sace Daliban Jami’a Mata…

Bugu da kari, an yi hakan ne domin samar musu da aikin yi da kuma rage rikicin da ke afkuwa a tsakanin makiyayan da monoma tare kuma da nufin mayar da ‘ya’yan fulani makarantar boko, su samu ilimin zamani.

Kungiyoyin fulani makiyaya biyu masu samar da madara wadanda suka fito daga Kananan Hukumomin Kubau da Chikun da ke Jihar Kaduna ne suka amfana da wannan shiri.

Har ila yau, shirin na daya daga cikin kokarin da take yi na bunkasa tattalin arzikin fulani makiyaya. Cibiyar bunkasa samar da madarar shanu (MBCF), karkashin shirin bunkasa sama wa matasa aikin yi ta hanyar noma da kiwo, wadda kungiyar ECOWAS ta dauki nauyi da wayar da kai.

Da take yin nata jawabin a wajen taron, Jami’ar Shirin Dakta Bilkisu Yusuf ta ce, an samar wannan da shiri ne domin rage yawan matasa marasa aikin yi a tsakanin fulani makiyaya da kuma tallafawa matansu.

Ta kara da cewa, shirin zai bai wa matasa makiyaya dama a kan yadda za su noma ciyawar shanu, a yayin kuma da za a bai wa matan makiyayan shanu; domin samar da wadatacciyar madara.

Bilkisu ta karfafawa matan guiwa kan su bai wa shirin goyon baya, musamman ganin yadda aka samar da shi domin tallafa wa rayuwarsu.

A karshe, wadanda suka amfana da wannan bita, sun yaba wa cibiyar bisa namijin kokarin da take yi na inganta rayuwa tare da alkawarin bayar da goyon baya, domin samun nasarar shirin a koda-yaushe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Masana Sun Bayar Da Mafita Kan Yadda Za A Samu Zaman Lafiya A Duniya

Masana Sun Bayar Da Mafita Kan Yadda Za A Samu Zaman Lafiya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version