Abdullahi Muhammad Sheka">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Jinjina Wa Mambobin WUCOBA 86 Bisa Halartar Taron Kungiyar

by Abdullahi Muhammad Sheka
January 4, 2021
in LABARAI
2 min read
WUCOBA
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tsofaffin Daliban Makarantar Koyon Harkokin Kasuwanci ta Wudil (WUCOBA) Aji na 1986 sun gudanar da taronsu, kamar yadda suka saba yi, inda shugaban kungiyar, Dr. Rabiu Nana, ya jinjina wa kokarin mambobin kungiyar bisa namijin kokarin da su ke yi wajen halartar irin wannan taro kowace shekara.

Dr. Rabiu Nana a cikin jawabinsa ya bayyana nasarorin da aka cimma cikin Shekarar data gabata, musamman shawarar daga wannan taro zuwa Shekara ta gaba Lokacin da ‘ya’yan kungiyar ke cika shekara 35 da kammala karatu, ziyarar zumunci, Ta’aziyyar ‘yan uwa da aka rasa, sai kuma Mota da dan wannan Kungiya kuma tsohon dalibin WUCOBA, Wakilin al’ummar Dawakin da Warawa a Majalisar wakilai ta Tarayya Alhaji Mustapha Bala Dawaki ya gwangwaje Kungiyar da motar aiki.

samndaads

Da ya ke gabatar da jawabinsa alokacin taron guda cikin jagororinmu wannan Kungiya Alhaji Suleiman Uba Gaya Wanda Kuma shi ne mataimakin shugaban Kungiyar Editoci na Kasa, shugaban Kamfanin Skylimit wanda ke buga Jaridar jamhuriyy da New Republican ya jinjana shugabannin wannan Kungiyar bisa jajircewar su wajen ganin wannan taro na gudanar yadda yadda kamata.

Haka kuma ya yaba da kokarin Alhaji Mustapha Bala Dawaki bisa gudunmawar kyautar mota ga wannan Kungiya, yace wannan abin alhairi ne kwarai da gaske, sannan ya bukaci da aka himmatuwa wajen kyautata zumunci a tsakaninmu.

Shi ma a nasa jawabin shugaban  makarantar WUCOBA Alhaji Abdallah Utai ya godewa  Tsoffin daliban nasa bisa hadin kai da kuma girmamawar da suke masa, saboda haka sai ya yi addu’ar fatan dorewar wannan hadin kai.

Taron ya samu halartar  wannan taro akwai tsohon Shugaban makarantar Alhaji Abdallah Utai, Hon. Mustapha Bala Dawaki, Dr. Suleiman Uba Gaya, Alhaji Aminu Aliyu, Alhaji Inusa Abdu Dambazau, Alhaji Auwalu Mu”azu da sauran dalibai ‘yan aji na Shekara ta 1986. Taron da ya gudana a dakin taro na Hukumar yawon bude ido ta Jihar Kano.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Nijeriya Ta Fitar Da Sabon Tsarin Canja Layin Waya

Next Post

Gidauniyar Ma’ajin Watari Na Kokarin Samar Da Wadatattun Likitoci Mata A Kano

RelatedPosts

FCTA

Hukumar FCTA Za Ta Tabbatar Da Ana Tsaftace Nama  A Mayankarta

by Abdullahi Muhammad Sheka
1 min ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Rsto ta aiwatar da sarrafa nama...

Fulani ‘Yan Nijeriya Ne, Babu Wanda Zai Iya Korarsu Daga Ondo – Miyetti Allah

Fulani ‘Yan Nijeriya Ne, Babu Wanda Zai Iya Korarsu Daga Ondo – Miyetti Allah

by Abdullahi Muhammad Sheka
4 hours ago
0

Shugaban Miyetti Allah na kasa, Kautal Hore, Bello Abdullahi Bodejo,...

FRSC

Shugaban Hukumar FRSC Ya Koka A Kan Yadda Ake Kai Wa Jami’ansa Hari

by Abdullahi Muhammad Sheka
11 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa Corps Marshal, na Hukumar Kiyaye Hadura...

Next Post
Gidauniyar Ma'ajin Watari

Gidauniyar Ma'ajin Watari Na Kokarin Samar Da Wadatattun Likitoci Mata A Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version