Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RIGAR 'YANCI

An Kaddamar Da Allurar Rigakafin Korona A Kebbi

by Muhammad
March 23, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Kebbi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk,

Gwamnatin Jihar Kebbi a karkashin jagorancin Kwamishinan ma’aikatar kiwon Lafiya kuma shugaban Kwamitin Kula Cutar Korona a Jihar ta Kebbi, Jafar Muhammad ya kaddamar da bikin fara karba alluran Rigakafin Korona a jihar kebbi.

An gudanar da bikin kaddamar da allurar ta riga- kafin ne a dakin gudanar da taro na Asibitin Kwararu ta gwamnatin Jihar Kebbi wato (Kebbi Medical Centre) da ke Kalgo a jiya, Inda aka cif medical Darakta na Kebbi Medical Centre da ke Kalgo, Dakta Abubakar Koko ya zama na farko da karbar allurar ta Rigakafin Korona sai kuma cif medical Darakta kuma sakataren din-din-din na Babbar Asibitin Tunawa da sarki Yahaya, Dakta Aminu Haliru Bunza wanda ya kasance mutun na biyu a duk fadin Jihar da suka karbi allurar Rigakafin Korona a jihar ta Kebbi a jiya.

Yayin kaddamar da allurar Rigakafin Korona a jihar, Kwamishinan ma’aikatar kiwon Lafiya kuma shugaban Kwamitin Kula da Cutar Korona Jafar Muhammad ya bayyana cewa” amada din Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya kaddamar da fara bayar da allurar Rigakafin Korona ga al’ummar jihar, amma an fara da ma’aikatar kiwon lafiya ne domin su ne ke Kula da marasa lafiya musamman Cutar Korona, inji Kwamishinan ma’aikatar kiwon lafiya yayin kaddamar da fara bayar da allurar Rigakafin Korona a Jihar Kebbi a jiya”.

Ya ci gaba da cewa” kafin kaddamar da wannan tsarin na bayar da allurar Rigakafin Korona a Jihar ta Kebbi mun gudanar da yekuwa da kuma fadakar wa ga al’ummar jihar ta hannun Sarakunan gargaji da kuma hakimawa na duk fadin Jihar wanda kan ya sanya al’ummar Jihar sun cire tsoro da kuma amincewa da cewa allurar Rigakafin bata da wata illa ga jikin dan’adam, inji Shi.

Haka kuma ya ce, “Idan aka kammala yiwa jami’an kiwon lafiya da sauran ma’aikatar kiwon lafiya zamu sanarwar yan jarida wadanda za a baiwa domin an yi tsari bisa ga rukunin jama’ar da za a baiwa alluran har zuwa ga al’ummar karkara, inji Kwamishinan ma’aikatar kiwon lafiya Jafar Muhammad”.

Daga karshe Kwamishinan Jafar Muhammad ya yi kira ga al’ummar jihar da su fito su karbi allurar Rigakafin bata da wata matsala domin sai da aka tabbatar da ingancinta kafin aka yadda da a yiwa al’umma ita,

SendShareTweetShare
Previous Post

Matawalle Ya Zama Khadimul Kur’an A Taron Mahaddata Alkur’ani Na Kasa

Next Post

Mun Gamsu Da Kwamitin Rikon APC Karkashin Buni – Hon. Mailambu

RelatedPosts

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by Sulaiman Ibrahim
2 weeks ago
0

Daga Abdullahi Muh’d, Kano Shugaban Gidauniyar ‘Charity’ mai rajin tallafa...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by Muhammad
2 weeks ago
0

Daga Zubairu M Lawal, A yayin da uwar jam'iyyar APC...

Shafukan

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by Muhammad
2 weeks ago
0

Daga Umar Faruk, Gwamnan Jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu, a...

Next Post
Buni

Mun Gamsu Da Kwamitin Rikon APC Karkashin Buni – Hon. Mailambu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version