Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home NOMA

An Kaddamar Da Rumbun Adana Doya Na Zamani A Nasarawa

by Sulaiman Ibrahim
March 17, 2021
in NOMA
2 min read
An Kaddamar Da Rumbun Adana Doya Na Zamani A Nasarawa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba

Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkar Alhaji Muhammad Sabo Nanono, ya kaddamar da rumbun adana Doya na zamani a jami’ar koyon darrisan aikin noma ta Keffi-Shabu- Lafia dake a jihar Nasarawa.
A cewar Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkar Alhaji Muhammad Sabo Nanono, rumbun zai iya adana daga tan 45 zuwa tan 50 na Doya kuma Ana san za a iya samun Irin na Doya da za a iya shuka wa a kadada 16.
Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkar Alhaji Muhammad Sabo Nanono ya bayyana hakan ne a jawabinsa a yayin kaddamarwar a makon da ya gabata.
Ministan Alhaji Sabo Nanono ya bayyana cewa yin amfani da ingantacce Irin noman Doya zai taimaka matuka wajen kara samar da kudaden shiga masu yawa ga manoman Doya da kuma kara habaka fannin a jihar ta Nasarawa harda Doyar da aka fitar zuwa kasuwannin duniya .
A cewar Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkar Alhaji Muhammad Sabo Nanono, gudanar da aikin a jami’ar zai taimaka matuka wajen kara gudanar da bincike, ilimantar wa, kara samar wa da manoma da kudade shiga masu yawa inda kuma aikin, zai kara samar da ayyukan yi kimanin 200.
“Gudanar da aikin a cikin wannan jami’ar zai taimaka matuka wajen kara gudanar da bincike, ilimantar wa, kara samar wa da manoma da kudade shiga masu yawa inda kuma aikin, zai kara samar da ayyukan yi kimanin 200.”
Shi ma a na sa jawabin a gurin taron taron, Shugaban Jami’ar jihar Nasarawa Farfesa Suleiman Mohammed ya sanar da cewa, za a yi amfani da Rumbun yadda ya da ce, musamman domin a karfafa kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi na daukaka gudanar da bincike kan fannin da kuma kara habaka fannin tattalin arzikin kasar.
A cewar Shugaban Jami’ar jihar Nasarawa Farfesa Suleiman Mohammed, gwamnatin jihar Nasarawa ya fitar da naira miliyan 35 domin kara inganta samar da ingantacce Irin na Doya a jihar.
“Za a yi amfani da Rumbun yadda ya da ce, musamman domin a karfafa kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi na daukaka gudanar da bincike kan fannin da kuma kara habaka fannin tattalin arzikin kasar.Bugu da karin, Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkar Alhaji Muhammad Sabo Nanono a wani aikin kuma tare da Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa na aikin gona Sanata Abdullahi Adamu, sun kai ziyarar aiki a wata gona ta zamani ta Shabu dake a karamar hukumar Kokona a cikin jihar ta Nasarawa.”
A yayin wannan ziyarar ta su, sun kuma nuna jin dadinsu kan samar da Rumbunan zamani na adana Doya da kungiyar kasa da kasa ta RIELA ta samar a gonar tare da kuma samar sa kayan aikin gona a jihar Nasarawa.
Har ila yau, Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkar Alhaji Muhammad Sabo Nanono, an kuma zagaya dashi wasu guraren da ake gudanar da aikin noma a jihar Nasarawa.
Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkar Alhaji Muhammad Sabo Nanono tare da Gwamnan jihar Nassarawa Abdulahi Sule a tun da farko, sun kai wata ziyarar aiki a gonar Sukari ta dangote mai fadin kadada 68,000 sake a yankin Tunga a jihar Nassarawa .

SendShareTweetShare
Previous Post

Cutar Dake Kama Tumatir Ta Bulla A Wasu Jihohin Arewacin Nijeriya

Next Post

Gwarzonmu Na Mako: Alhaji Nasiru Muhammad (2)

RelatedPosts

Noma

Aikin Noma Na APPEALS Ya Kawo Ci Gaba A Legas -Manoma

by Muhammad
16 hours ago
0

Daga Abubakar Abba, Fannin aikin noma ako wacce kasa na...

Masara

Batun Masana’antun Kiwon Kajin Da Daukin CBN Na Samar Da Tan 300,000 Na Masara

by Muhammad
16 hours ago
0

Daga Abubakar Abba, A kimanin watanni sha biyar da suka...

Har Yanzu Nijeriya Na Shigo Da Madara Kashi 60 Cikin Dari – Nanono

Har Yanzu Nijeriya Na Shigo Da Madara Kashi 60 Cikin Dari – Nanono

by Sulaiman Ibrahim
7 days ago
0

Daga Abubakar Abba Ministan ma’aikatar aikin gona da raya karkara...

Next Post
Gwarzonmu Na Mako: Alhaji Nasiru Muhammad (2)

Gwarzonmu Na Mako: Alhaji Nasiru Muhammad (2)

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version