An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana'o’i A Kano
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana’o’i A Kano

byAbdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Noma

An bayyana shirin Gwamnati Na Kano CARRES da cewa shi ne shirin da yafi sauran shirye shiryen da ake bijiro dasu da sunan tallafin saukakawa jama’a radadin matsin rayuwa da jama’a ke fama da ita tun bayan faruwar Annobar Korona wadda tayi sanadin durkushewar tatalin jama’a.

Shugaban Hukumar Kano CARES na Jihar Kano Alhaji Rufa’I ne yabayyana haka alokacin da yake zagawa da babban sakataren ma’aikatar gona na Jihar Kano Alhaji Salisu Tahir alokacin shirin da ake na kaddamar da tallafin kayan Noma ga daruruwan matasa maza da mata a Jihar Kano.

  • Tinubu Ya Kori Shugaban Hukumar NASENI Bayan Wata 3 Da Nadinsa
  • Rage Radadin Cire Tallafi: Gwamnati Ta Baiwa  Kowacce Jiha Naira Biliyan Biyu A Kashin Farko

Alhaji Rufa’I ya shaidawa Babban sakataren Ma’aikatar gonan na jIhar Kano cewar wannan hukuma ta himmatu kamar yadda aka bata cikin kudin tsare tsaren wannan hukuma na samar da tallafi kamar bayar da injunan nika, injin malkade, injin ban ruwa mai amfani da hasken rana, kiwon Kaji, samar da hanyoyi a karkara da kuma gina wuraren kewayawa a kasuwanni da wuraren taruwar al’umma.

Hakazalika shugaban hukumar ta Kano CARES  ya bayyanawa mahalarta taron irin yadda majalisar mahaddata alkur’ani suma suka shigo cikin tsarin, musamman ganin suna da kyakkyawan shirin rage kwararar almajirai daga kauyuka zuwa manyan birane tare da kokarin magance matsalar barace barace wadda a halin ke neman zama wata barazana a jihar Kano, don haka sai ya tabbatar da cewa yanzu haka shirye shirye sunyi nisa na sake samar da wani rukunin al’umma da suma ake fatan zasu rabauta da wannan tallafi da Gwamnatin Kano ke saukewa al’ummarta.

Da yake jawabi alokacin da yake ganewa idonsa irin kayayyakin da hukumar ta samar domin rabawa al’umma musamman abinda ya shafi noma, kiwo da sana’o’in dogaro da kai, Dakta Farouk Kurawa ya bayyana farin cikinsa tare da jinjinawa kokarin wannan hukuma wadda yace babu shakka ya fahimci yadda jama’a ke alfahari da ayyukan wannan hukuma ke nuni da kyakkyawan alhairan da ke kunshe cikin manufofi da aikace aikacen hukumar ta Kano CARES.

Shima da yake duba kayayyakin da hukumar Kano CARES ta tanada domin ci gaba da rabawa jama’a, babban sakataren ma’aikatar gona na Jihar Kano Alhaji Salisu Tahir ya nuna gamsuwa da irin kalaman da yaji daga bakin wadanda suka amfana da alhairan wannan hukuma ta Kano CARES, musamman kan batan smaar da hanyoyi a karkara, inda wasu da suka amfana daga Kananan Hukumomi Gazawa da Kura suka bayyana farin cikin al’umarsu bis aaikin hanya da wannan hukuma ta shimfada masu a yankunansu.

Alhaji Salisu Tahir ya jinjinawa kokarin shugabannin hukuma tare da rokonsu da su kara himma wajen sauke nauyin da aka dora masu, sannan kuma ya bukaci wadanda suka amfana da wadanann tallafi iri daban daban da suyi kyakkyawan amfani dashi, domin ganin nan gaba kadan suma sun zama suna cikin wadanda da za su taimaka wa sauran al’umma. A karshe ya yi addu’ar Allah ya sawa damunar mu albarka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Next Post
Gwamnan Kaduna

Gwamnan Kaduna Ya Bude Masaukin Dalibai Mai Gado 400 Da Ofishin Hukumar Raya Birnin Zariya

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version