An Kama Mutum 89 Da Ake Zargi Da Fashi Da Dillancin Muggan Kwayoyi A Kano
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Mutum 89 Da Ake Zargi Da Fashi Da Dillancin Muggan Kwayoyi A Kano

byRabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
1 year ago
Fashi

Rundunar ‘yansanda a Jihar Kano, ta ce ta samu gagarumar nasara a kokarinta na tabbatar da tsaron lafiyar jama’a da kuma rigakafin aikata laifuka.

 

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Salman Dogo Garba, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a shalkwatar ‘yansandan da ke Bompal.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas
  • Da Gangan Aka Rikirkita Tsarin Zaben Nijeriya Domin A Samu Damar Yin Magudi – Sanata Ndume

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya wakilta, CP, ya ce rundunar ta samu nasarar cafke wasu miyagun mutane 89 da suka hada da ‘yan fashi da makami 15, wasu 10 kuma da ake zargin dillalan miyagun kwayoyi, da kuma mutum daya da ake zargi da safarar mutane.

 

Har ila yau, ya bayyana cewa, ‘yansandan sun samu nasarar kubutar da mutum biyu da aka yi garkuwa da su.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yan sandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Bakardin Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

Bugu da kari, ya kara da cewa, matakin da rundunar ta dauka na fara gudanar da ayyukan al’umma masu inganci, sun hada da gudanar da ayyukan leken asiri, da kuma sintiri na gani ba dare ba rana, wanda hakan ya haifar da sakamako mai kyau, inda aka gurfanar da mutane 43 da ake tuhuma a gaban kotu, yayin da wasu 46 ke fuskantar bincike.

 

Kiyawa ya jaddada cewa rundunar ta fahimci muhimmancin hadin kan al’umma da hadin gwiwa wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafofin yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.

 

Ya bukaci mazauna yankin da su bai wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro hadin kai, da kuma shiga cikin aminci a cikin bukukuwan, tare da mutunta ‘yancin wasu.

 

Shugaban ‘yansandan ya kuma jajantawa iyalan ‘yansandan biyar da suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a ranar 23 ga watan Satumba 2024, ya kuma yaba da addu’o’i da goyon bayan da aka bai wa iyalan wadanda suka rasu da wadanda suka jikkata.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yansandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafafen yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version