Haruna Akarada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

An Karrama Fitattun Mutane A Bikin Ranar Nakasassu A Kano

by Haruna Akarada
December 7, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Fitattun Mutane
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A ranar Larabar da ta gabata ne Majalisar Dinkin Duniya ta shirya wa masu bukata ta musamman taro dangane da girmama su da karrama wasu fitattin mutane da su ke bayar da gudunmawa ga wadannan bayin Allah.

Kadan daga cikin masu bayar da gudunmawar akwai Ballo isa Bayaro da Alhaji Sule Lamido, tsahon gwamnan Jihar Jigawa, sai shugaban karamar hukumar Gwale Khalid Ishak da Alhaji Garba Baban Ladi, sai Kawu Idiris Hausawa da Hajiya Sadiya Adamu.

samndaads

An yi wannan taro ne a dakin karatu na Murtala Muhammad da ke Kano.

Alhaji Bello Isa Bayero ya yi kira ga ’yan siyasa da masu mulki da masu hannu da shuni da su dinga taimaka wa wadan nan bayin Allah masu bukata ta musamman, domin su ma mutane ne kamar kowanne mutum, amma wasu abubuwan ba za su iya ba sai an taimaka mu su.

Tasiu Shehu Garko shi ne babban mataimaki ga gwamnan jihar Kano, inda ya isar da sakon gwamnati a wannan taro kan tattalin arzikin masu bukata ta musamman sakamakon Korona

Ya ce, kiran gwamnati shi ne, masu bukata ta musamman su garzayo su amfana da ilimi kyauta tun daga firamare har jami’a.

“Kuma zuwana wannan guri mai girma gwamna bai bari na zo haka kawai ba. Ya bada kayan abinci a ba su, kuma batun da gwamna ya yi na ilimin mai bukata ta musamman kyauta ne, ba shi kadai ba, a’a, hard a dansa, kuma duk matakan da za a kawo yaro mun dauki wannan.”

Shi ma Injiniya Musa Muhammad Shaga, shugaban gamayyar kungiyoyi masu bukata ta musamman ya bayyana watsi da a ke yi da su, ya ce, wannan ba shi da abinda ya fi damun sa kamar sa.

Ya ce, akwai yaransu da da dama da su ka gama karatu, amma maganar aiki babu. Amma ya ce, maganar karatu kyauta ne wannan babu matsala tun daga locacin Malam Ibrahim Shekarau ya zuwa yanzu babu abinda ya tsaya, amma maganar aiki shi ne akwai matsala.

“Da a na daukar aiki, to duk wannan surutun bara da an daina,” in ji shi.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Nijeriya Ta Amince Da Biliyan N120.7 Don Hanyoyi Da Motocin Sintiri

Next Post

Kasafin 2021 Zai Karfafa Cigaban Jihar Gombe, In Ji Inuwa Yahaya

RelatedPosts

IPOB

IPOB Ta Bayyana Dalilin Arangamarta Da Sojoji

by Haruna Akarada
53 mins ago
0

A jiya ne 'Yan asalin Biafra (IPOB) da aka haramta...

NDLEA Ta Damke Mutum 544 Bisa Zargin Fataucin Kwayoyi A Borno

NDLEA Ta Damke Mutum 544 Bisa Zargin Fataucin Kwayoyi A Borno

by Haruna Akarada
55 mins ago
0

Shugaban hukumar yaki da sha tare da fataucin miyagun kwayoyi...

‘Yan Sanda Sun Ceto Yara Takwas, Sun Kama Masu Juna-biyu A Anambara

‘Yan Sanda Sun Ceto Yara Takwas, Sun Kama Masu Juna-biyu A Anambara

by Haruna Akarada
55 mins ago
0

An kama wasu mata takwas, ciki har da mata masu...

Next Post
Inuwa Yahaya

Kasafin 2021 Zai Karfafa Cigaban Jihar Gombe, In Ji Inuwa Yahaya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version