An Kashe Mutane 5000, An Sace 7000 Cikin Shekara 1 A Mulkin Tinubu - Bincike
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Mutane 5000, An Sace 7000 Cikin Shekara 1 A Mulkin Tinubu – Bincike

bySadiq
1 year ago
Tinubu

Wani bincike da kafafen yada labarun Nijeriya da kungiyoyi suka gudanar ya nuna cewa ayyukan ta’addanci sun hallaka mutane 4,500 yayin da aka yi garkuwa da mutane 7,000 cikin shekara guda a karkashin mulkin Bola Ahmed Tinubu.

Kungiyar ACLED mai tattara kididdigar kisa ko kuma mutanen da aka yi garkuwa da su ta ce bayananta sun nuna cewa mutane 4,556 ne suka rasa rayukansu sai wasu 7,086 da aka yi garkuwa da su a tsakanin ranakun 29 ga watan Mayun bara zuwa 11 ga watan Mayun da muke ciki.

  • Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano Ta Haramta Zanga-zanga A Jihar
  • Ɓata-gari Sun Lalata Hasumiyar Wutar Lantarki 3 Na Layin Biu-Damboa

A lokacin jawabinsa na ranar 29 ga watan Mayun 2023 lokacin da aka rantsar da shi, Tinubu ya sha alwashin tunkarar matsalolin ta’addanci da kuma rashin tsaro gadan-gadan.

Wannan ba shi ne karon farko da shugaban ke yi wa ‘yan Nijeriya alkawari kan magance matsalar tsaro ba.

Hakan ya kasance tamkar waka a manyan batutuwan da yake nanatawa a wajen yakin neman zabe.

Sai dai, shekara daya yau cif da darewarsa karagar mulki, a iya cewa babu wani sauyi na azo a gani a bangaren tsaro, illa ma dai sake sabon salon kai hare-hare da ‘yan bindiga musamman a Arewacin kasar nan ke kai wa.

Ita kuwa kungiyar Boko Haram tsagin Ansaru ke ci gaba da samun karfi tare da kai hare-hare a yankin Arewa Maso Gabas.

Cikin makon da ya gabata sai da mahara suka yi garkuwa da mutane 160 a Jihar Neja, a wani hari da ba a taba ganin irinsa a jihar ba.

Duk da alkawuran da shugaban ya yi, da kuma ikirarin yaki da ta’addanci da manyan hafsoshin tsaron kasar ke yi na yaki da ta’addanci, har yanzu matsalolin rashin tsaro na ci gaba da zama ruwan dare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Dokar Dawo Da Tsohon Taken Kasa

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version