An Kashe Mutum 4 A Wani Rikici Tsakanin Hausawa Da Kabilar Lunguda A Adamawa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Mutum 4 A Wani Rikici Tsakanin Hausawa Da Kabilar Lunguda A Adamawa

byMuh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
An

Hukumomi sun tabbatar da mutuwar mutum hudu a wani rikicin da ya barke tsakanin Hausawa mazauna Lafiya da ‘yan kabikar Lunguda a garin Lafiya cikin karamar hukumar Lamurde ta jihar Adamawa.

Mazauna garin sun tabbatar da cewa rikicin ya barke ne akan gonaki, inda suka bayyana cewa mutane da dama sun mutu sakamakon barkewar rikicin.

  • 2023: Gwamnonin APC Daga Arewa Sun Kafe Kai Da Fata Sai Dan Kudu Ya Yi Takara
  • Adamu Ya Kori ‘Yan Jarida Daga Ofishin APC Bayan Tutsun Da ‘Yan Jam’iyyar Suka Tayar

Maista Bulus Daniel, shi ne shugaban karamar hukumar Lamurde, ya tabbatar da mutuwar mutum biyar biyo bayan tashin rikicin da safiyar ranar Litinin.

Wani mazaunin yankin ya ce “Ni bana garin amma ina hanyar dawo wa, duk wani labarin da yake fitowa daga yankin ka dauke shi tamkar karya, jami’an tsaro basu bada cikakken rahoto ba tukuna.

“Abinda zan iya shaida maka shi ne kusan mutum 4 ne suka rasa rayukansu, amma a hukumance bamu kai ga kididdige adadin mutanen da lamarin ya shafa ba” inji Bulus.

Wani ganau, da ya bukaci a sakaya sunansa, ya shaidawa LEADERSHIP Hausa cewa “kwanakin baya mutanenmu su nje gona, sai aka sassari wasu mutane mu kuma muka sanarwa jami’an tsaro da shugaban karamar hukuma.

“Ya bamu hakuri kada mu dauki wani mataki, to yau wasu sun fita gona sai mutanen Lunguda suka kashe mana wani mutum mai suna Sani, shi ne ya kawo rincabewar rikicin, yanzu an kashe mana mutum biyu, muna da labarin akwai wasu biyu ko uku da aka kashe a wajan gari.

“Mun kai kuka gun hukumomi amma har yanzu ba su iya daukar matakin shawo kan matsalar ba, kuma kullum mutanenmu ake kashewa” inji Mazauna yankin.

Itama rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da rikicin, sai dai tace kura ta lafa.

DSP Suleiman Ngoroji, shi ne jami’in hulda da jama’a na rundunar, ya ce “an jibgi runduna ta musamman a yankin domin dakile rikicin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post

12 Le plus facilement utile Sites Comme Craigslist Personals (100 pour cent gratuit Tests)

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version