An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

Sunan Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yi Batan-dabo Cikin Kwamitin

byKhalid Idris Doya
3 years ago
PDP

An nada mamba kuma jigo a jam’iyyar PDP sannan Sanatan da ke wakiltar mazabar Enugu ta Gabas, Chimaroke Nnamani a cikin kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023 da ke karatowa.

Hakan na kunshe cikin jerin sunayen da aka fitar a daren ranar Juma’a inda aka nemi sunan mataimain shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo sama da kasa cikin jerin kwamitin yakin zaben na Tinubu aka rasa, inda aka rawaito cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya umarci mataimakin nasa da ya maida hankali kawai wajen gudanar da mulki.

  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS
  • Dakarun Kasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Wanzar Da Zaman Lafiya

Kazalika, jam’iyyar ta ki sanya sunan tsohon kakakin majalisar dokokin tarayya, Yakubu Dogara, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal; tsohon ministan ilimi, Chukwuemeka Nwajiuba da dan-gani-kashenin Tinubu, Adebayo Shittu, wadda ya jagoranci manyan kungiyoyin goyon bayan Tinunu, ‘Asiwaju Tinubu-Shettima Coalition for Good Governance’ dukka babu sunayensu.

A wata sanarwar da jami’in watsa labarai na kwamitin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, Festus Keyamo (SAN) ya fitar, ya ce an cire sunan Osianbajo da sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha daga cikin kwamitin yakin zaben ne sakamakon umarnin da shugaba Buhari ya bayar na cewa su maida hankali wajen gudanar da harkokin mulkin Nijeriya a halin yanzu.

Jerin kwamitin yakin zaben mai mutum 422 da sakataren kwamitin yakin zaben, Hon. James Faleke ya fitar, kuma an gano cewa wasu jerin fitattun jigogin jam’iyyar babu sunayensu a ciki.

Kazalika, shugaba Muhammadu Buhari shine shugaban kwamitin yakin zaben, Bola Ahmed Tinubu kuma shine mataimakin shugaba na kwamitin yakin zaben APC, yayin da kuma gwamnan jihar Filato, Simon Bako Lalong ya kasance darakta-janar yakin neman zabe na Tinubu.

Tsohon shugaban jam’iyyar, Kwamared Adams Oshiomhole shine aka ayyana a matsayin mataimakin darakta-janar nay akin zaben a sashin ayyuka, sanna akwai sunayen gwamnoni, ministoci, ‘yan majalisu, jakadu, da wasu jiga-jigai cikin kwamitin yakin zaben na Tinubu.

A sanarwar ta Keyamo, ya ce sabanin yadda wasu rahotonni ke yawo na cewa an cire sunayen wasu na kusa-kusan Buhari cikin kwamitin yakin zaben da kokarin nuna cewa akwai Baraka a jam’iyyar, ya ce sam ba haka zancen yake ba, illa dai ya nuna cewa Buhari ne ya umarci Osinbajo da Boss da su maida hankali wajen gudanar da mulki.

“A matsayin jam’iyyar da ta san meye take yi da gwamnatin da ta san meye take yi, ba zai yiyu a kwashe dukkanun manyan jami’an gwamnati a ce su bar ayyukansu su shiga kwamitin yakin zabe ba. APC ita ce ke da ikon jan ragamar Nijeriya har zuwa ranar 29 ga watan Mayun 2023, don haka akwai bukatar wasu su fi maida hankali wajen gudanar da harkokin mulki ba zallar yakin zabe ba.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version