Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

An Nada Yusuf Dauda Sarautar Turakin Kofa

by
1 year ago
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Yusuf Dauda
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Mai girma Sarkin Kofa, Alhaji Nasiru Adamu Kofa, ya nada Alhaji Yusuf Dauda Kofa sarauta a matsayin Turakin Kofa ta Jihar Kano a ranar Lahadin da ta gabata. Alhaji Yusuf Dauda Kofa, wanda shi ne shugaban kungiyar bangaren ‘yan kasuwa masu sayar da citta da Tafarnuwa a kasuwar Mile 12.

Kafin Alhaji Yusuf Dauda Kofa ya samu wannan sarauta dai ya taba rike mukamai da dama a kasuwar ciki har da wannan mukamin da yake rike da shi a halin yanzu.

Taron nadin sarautar wanda ya gudana a harabar fadar magirma sarkin Kofa ya samu halartar shugaban kasuwar mile12 Alhaji Shehu Usman Jibirin Samfam da tawagarsa ta shugabannin bangarorin kasuwar da sauran al’umma da suka fito daga sassa daban-daban na Kano, Kaduna, Legas, Jos da katsina baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Makada, mawaka da sauran abubuwan da suka gudana na ban shaawa a wajen taron. Babban bako a wurin taron shugaban kasuwar ta mile I2, Alhaji Shehu Usman Jibirin da sakataren kasuwar Alhaji Idiris Balarabe Legas da ma’aji Alhaji sa’idu Usaini sarina da shugaban ciyamomin kasuwar Alhaji Abdullahi Tukur Kura, da Abdulgiyasu Sani Rano, shugaba ‘yan kasuwar tumatiri, sauran sun hada da shugaban bangaren karas da kabeji Alhaji Bala Yaro hunkuyi, da iyayen kasuwar shugaban kungiyar dattawan kasuwar Alhaji isa Mohammed da Alhaji Habu Faki Garkuwan Faki, da Alhaji Abdulwahab tsoho Babangida, da sauransu.

Masu masaukin baki su ne Alkalin kungiyar bangaren citta da tafarnuwa Alhaji Tasi’u danbaba, da sakatarensu Sunusi Abubakar shi ka zariya. Da yake tsokaci a matsayinsa na uba kuma wanda yaba Alhajl Yusif Dauda Kofa, ya ce wannan sarauta an nada shi a wannan matsayi domin yaro ne mai hankali da biyayya, da kuma sanin ya kamata, da sauran kyawawan halaye masu kyau, a kan haka ya ga cewar ya bashi sarauta ta.

A cewarsa tun yana yaro karami yake tare da kyawawan dabiu masu kyau wadanda za su koya wa matasa na baya masu tasowa tarbiyyar tagari shi ma ana sa tsokacin shugaban kasuwar ta Mile I2 Alhaji Samfan ya nuna farin cikinsa a game da nadin da fatan Allah ya yi yi masa jagora a game da al amari kuma ya zaunar da kasar lafiya baki daya.

Alhaji Yusuf Dauda dai ya gode wa Sarkin Kofa bisa wannan nadi da ya yi masa, yana mai cewa, babban karamci ne a gare, wanda kuma a ya ce zai yi iyaka kokarinsa ya ga ba wa marada kunya.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Kwamitin Kasuwar Mile-12 Ya Fara Ziyarar Jaje Da Ta’aziyya Ga Manoman Arewa

Next Post

Matsalar Ruwan Sha A Lokoja Za Ta Zama Tarihi, Cewar Injiniya Abdulsalam

Labarai Masu Nasaba

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by
1 year ago
0

...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by
1 year ago
0

...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by
1 year ago
0

...

Kebbi

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by
1 year ago
0

...

Next Post
Injiniya Abdulsalam

Matsalar Ruwan Sha A Lokoja Za Ta Zama Tarihi, Cewar Injiniya Abdulsalam

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: