Abba Ibrahim Wada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

An Raba Jaddawalin Wasannin Neman Cancantar Zuwa Kofin Duniya Na Turai

by Abba Ibrahim Wada
December 9, 2020
in WASANNI
2 min read
Kofin Duniya Na Turai
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tawagar ‘yan wasan kasar Ingila za ta fafata da tawagar kasar Poland a rukuni na tara a wasannin neman shiga gasar kofin duniya da za a yi a 2022 a kasar Katar kamar yadda aka raba jadawalin ranar Litinin.

Sauran wadanda ke cikin rukunin sun hada da Hungary da Albania da Andorra da kuma San Marino sannan tawagar Wales za ta kara da Belgium, wadda ta fitar a gasar nahiyar Turai ta Euro 2016, inda za su kara a rukuni na biyar.

samndaads

Ireland ta Arewa tana rukuni na biyar da ya kunshi kasashen Italy da Switzerland da Bulgaria da kuma Lithuania ita kuma Scotland za ta kece raini da Denmark da Austria da Israel da tsibirin Faroe da kuma Moldoba a rukuni na shida.

Ita kuwa Jamhuriyar Ireland za ta yi gumurzu da Portugal da Serbia da Ludembourg da kuma Azerbaijan sannan za a fara wasannin ne tsakanin watan Maris zuwa Nuwambar shekara ta 2021, sannan a buga wasannin cike gurbi daga Maris din 2022.

Rukuni na uku: Italy da Switzerland da Ireland ta Ireland da Bulgaria da kuma Lithuania.

Rukuni na biyar: Belgium da Wales da Jamhuriyar Czech da Belarus da kuma Estonia.

Rukuni na shida: Denmark da Austria da Scotland da Israel da tsibirin Faroe da kuma Moldoba.

Rukuni na tara: Ingila da Poland da Hungary da Albania da Andorra da kuma San Marino.

Sakamkon yanayi na zafi a Katar, gasar kofin duniya da kasar za ta karbi bakunci za’a fara daga 21 ga watan Nuwamba zuwa 18 ga Disambar 2022 saboda hakan zai sa gasar ta zama ta farko da za’a gudanar da ita ba a watan Mayu ko Yuni ko kuma Yuli ba.

Za kuma a gudanar da wasannin a kwanaki 28 da ake sa ran kasashe 32 za su kece raini a filaye takwas a birane biyar da za su karbi bakuncin gasar inda tuni kasar tana ci gaba da shirye shiryen ganin ta samu nasarar gudanar da gasar.

Tawagar kwallon kafa ta Faransa ce ke rike da kofin duniya da ta lashe a kasar Rasha, kuma na biyu da take da shi a tarihi har ila yau ana ganin tana da warfin da zata iya sake lashe kofin a kasar ta Katar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kungiyoyi Biyar Za Su Iya Lashe Gasar Firimiyar Bana – Klopp

Next Post

Tsaro: Matasan Arewa Sun Nemi A Kori Shugabannin Sojoji Da Ministan Ayyuka

RelatedPosts

Alcantara

Alcantara Bai Dace Da Salon Wasan Liverpool Ba –Dietmar Hamann

by Abba Ibrahim Wada
10 hours ago
0

Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Liverpool, Dietmar Hamann,...

Aguiro

Muna Bukatar Aguiro Ya Dawo Wasa – Guardiola

by Abba Ibrahim Wada
10 hours ago
0

Kociyan kungiyar kwallon kafa Pep Guardiola ya ce lallai Manchester...

Wenger Ozil

Wenger Ya Jinjina Wa Ozil

by Abba Ibrahim Wada
10 hours ago
0

Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, Arsene Wenger,...

Next Post
Shugabannin Sojoji

Tsaro: Matasan Arewa Sun Nemi A Kori Shugabannin Sojoji Da Ministan Ayyuka

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version