An Rage Hukuncin Kwashe Maki 10 Da Aka Yi Wa Everton
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rage Hukuncin Kwashe Maki 10 Da Aka Yi Wa Everton

byAbba Ibrahim Wada
2 years ago
Everton

An rage hukuncin da aka yanke wa Ebeton kan saba wa dokokin hada-hadar kudi ta gasar Premier daga maki 10 zuwa shida bayan nasarar da kungiyar ta yi a karar da ta daukaka.

An gurfanar da kungiyar a gaban wata hukuma mai zaman kanta a watan Maris bisa zargin tafka laifukan a kakar wasa ta 2021 zuwa 20022, kuma da farko an cire mata maki 10 a watan Nuwamban 2023.

  • Pogba Zai Ɗaukaka Ƙara A Kan Dakatar Da Shi Daga Buga Ƙwallo Na Tsawon Shekaru 4
  • Liverpool Ta Lashe Kofin Carabao Karo Na 10 Bayan Doke Chelsea A Wembley

Ragin da aka yi kan hukuncin zai sa Everton ta kasance da maki 25 sannan ta koma mataki na 15 a teburin Premier bayan wata sanarwa da hukumar tafiyar da gasar Premier League ta fitar inda ta bayyana cewa “Hukumar daukaka kara mai zaman kanta ta yanke cewa hukuncin da Everton FC za ta fuskanta kan keta ka’idojin kasuwanci na Premier League na kakar 2021 zuwa 2022, zai zama cire mata maki shida nan take.

Hukumar ta ce wannan ya biyo bayan daukaka karar da Everton ta yi na hukuncin da wata hukuma mai zaman kanta ta yanke a watan Nuwamba 2023 na cire maki 10 saboda keta dokokin.

Sanarwar ta kara da cewa wannan hukuncin da aka sake wa fasali zai fara aiki ne nan take kuma za a sabunta teburin Premier daga lokacin da aka yi hukuncin domin yin la’akari da hakan.

Hukuncin farko da aka yanke wanda shi ne mafi girma a tarihin gasar Premier – ya sa Everton ta rikito daga mataki na 14 zuwa 19 a kan teburi amma kuma duk da haka kungiyar ba ta karaya ba, ta dage wajen samun nasara a wasanni.

Har Yanzu Everton da Nottingham Forrest Ba Su Da Makoma Amma kuma har yanzu kungiyoyin kwallon kafa na Everton da Nottingham Forest ba za su iya sanin makomarsu ba har sai bayan kammala gasar Premier ta bana saboda bincike da ake ci gaba da yi.

Everton na murnar rage hukuncin da aka yanke mata daga maki 10 zuwa maki shida bayan ta daukaka kara amma duk da haka Everton da Forrest na da sabbin tuhume-tuhume da ake yi masu sakamakon keta dokokin hada-hadar kudi na gasar Premier League, inda za a gurfanar da kungiyoyin biyu a gaban wani kwamiti mai zaman kansa a farkon watan Maris, kuma dole ne su tabbatar da hukunci kafin ranar 8 ga Afrilu.

Idan har an yanke hukuncin cire maki, kungiyoyin biyu na da kwanaki bakwai domin daukaka kara, sannan dole ne a tabbatar da sakamakon wannan lamari kafin babban taron gasar Premier League wanda za a gudanar a ranar 24 ga watan Mayu, kwana biyar bayan an kammala kakar wasa ta bana.

Hakan na nufin cewa idan har kugiyoyin biyu sun fuskanci hukuncin cire maki suna iya samun kansu a matakin gasar ‘Championship’ ko da kuwa sun kai labari sakamakon wasannin da suka buga a kakar wasa ta bana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
Xi Ya Jaddada Bukatar Raya Sabon Makamashi Mai Inganci A Kasar Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Raya Sabon Makamashi Mai Inganci A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version