Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Alumni Na Isa Mustapha Agwai A Nasarawa

by Muhammad
January 12, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Alumni
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Zubairu M Lawal,

Kungiyar Alumni dake makarantar kimiyya da fasaha ta Isa Mustapha Agwai dake Lafia jihar Nasarawa ta ranatsar da sabbin Shugabannin a ranar Litinin 11 ga Janairu, 2021.

samndaads

Bayan zaben sabbin Shugabannin da aka gudanar a ranar 12 ga watan Dusambar shekarar 2020.

Kungiyar ta zabe sabbin Shugabannin su takwas bisa yadda tsarin mulkin kungiyar ya tabbatar da mukaman Shugabannin kungiyar.

Bayan rantsar da sabbin Shugabannin, tsohon Shugaban kungiyar Jamilu Abubakar ya nuna godiya da yadda ya’yan kungiyar suka gudanar da zaben sabbin Shugabannin bisa tsari da inganci.

Ya kuma yi fatan sabbin Shugabannin zasu cigaba da jan ragamar kungiyar bisa tafarkin gaskiya da rikon amana.

Ya kuma yi godiya ga membobin kungiyar saboda goyon bayan da suka basu na gudanar da nasu mulkin zuwa adadin karewar su ga jagoranci. Daga bisani ya mika ragamar kundin tsarin mulki ga sabon shugaba.

Shi ma sabon shugaban kungiyar Mista Ogbole Arenya ya yi godiya ga Membobin kungiyar da suka bashi dama domin jagorantar su.

Ya kuma yabawa tsofin Shugabannin kungiyar saboda yadda suka jajirce har kungiyar ta kafu da kafarta.

Ya kuma godewa Hukumar zaben da ta gudanar da zaben bisa inganci.

Yayi kira ga sauran membobin kungiyar dasu zo a hada kai a tafi tare domin cigaban wannan kungiyar da Makarantar kimiyya da fasaha ta Isa Mustapha Agwai.

Ya ce za su kawo sauyi mai mahimmanci ga wannan makarantar da hadin kai domin gudanar da ayyuka tare da Shugabannin makaranta da duk wani fanni na jagororin dake makarantar harma da bangaren dalubai.

Ya kara da cewa burinsu tabbatar da adalcine ga kowa da kowa dake kungiyar dama wannan makaranta

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Ya Daga Likafar Misilli Zuwa Darakta Janar Kan Yada Labarai

Next Post

Akwai Bukatar Koyi Da Sardauna Bagadawa Kan Ba Marayu Jari – Dallatun Bichi

RelatedPosts

Sojoji Sun Tarwatsa Sansanin Boko Haram A Borno 

by Sulaiman Ibrahim
16 hours ago
0

Rundunar sojan Najeriya ta bayyana samun nasarar tarwatsa sansanin da...

Jam'iyyar Adawa

Jam’iyyar Adawa Ta PDP Ta Yi Babban Kamu A Kebbi

by Sulaiman Ibrahim
16 hours ago
0

Jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Kebbi tayi babban kamu...

Majalisar Malamai

Majalisar Malamai A Kogi Ta Raba Zakkar Miliyan N2.5 Ga Mutum 63

by Sulaiman Ibrahim
16 hours ago
0

Majalisar Malamai ta Najeriya,reshen jihar Kogi(Council of Ulama) ta rarraba...

Next Post
Bagadawa

Akwai Bukatar Koyi Da Sardauna Bagadawa Kan Ba Marayu Jari – Dallatun Bichi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version