Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Sake Kama Sowore Bisa Shirya Zanga-zanga A Cikin Dare

by Khalid Idris Doya
January 2, 2021
in LABARAI
2 min read
Sowore
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Dan gwagwarmayar siyasar nan kuma tsohon dan takarar shugaban kasa, Mista Omoyele Sowore dai ya fuskaci fushin jami’an tsaro a jajibiren sabuwar shekara inda suka cafke shi a Abuja bisa jagorantar zanga-zangar cikin dare domin kalubalantar gwamnatin tarayya.

Sowore dai shi ne mawallafin kayar hada labarai ta Sahara Reporters, jami’an ‘yan sanda ne suka kama shi bisa jagorantar zanga-zanga a birnin tarayya Abuja bisa kiran samar da rayuwa mai inganci ga ‘yan kasa.

samndaads

An kira layukan Sowore a safiyar jiya Juma’a amma dukkanin layukansa biyun ba su shiga. Har dai zuwa yanzu ba a samu adadin yawan wadanda aka kama su tare da Sowore din ba.

Har zuwa lokacin hada wannan labarin ba a jiyo komai daga bakin jami’in watsa labarai na ‘yan sanda Mista Frank Mba ba.

Zanga-zangar dai wacce suka fito da ita, da bukatu daban-daban dukka dai da suke nuna rashin gamsuwa da salon mulkin gwamnatin Buhari.  Sun fara ne da karfe 11:30 na daren kashegarin sabowar shekara da zimmar za su cigaba da zanga-zangar har zuwa jiya farkon sabuwar shekara.

Sowore ya bukaci masu shiga zanga-zangar da su fito da ababen da za su nuna kiranye-kiranyen da suke da su domin bukatar samar da sauyi da canji.

‘Yan sanda sun tarwatsa zanga-zangar a yankin Gudu da ke Abuja, inda suka kamu wasu daga cikin masu zanga-zangar.

Wanda har zuwa aiko da labarin nan su na karkashin kulawar ‘yan sandan.

Zanga-zangar mai neman samar da rayuwa mai inganci da kuma neman inganta aikin tsaro tare da sukar gwamnatin Buhari bisa gazawa.

Tunin dai wasu kungiyoyi suka fara kiran a sake Sowore.

Idan za ku iya tunawa dai a farko an taba tsare Mista Sowore na tsawon sama da kwanaki 100 a shekarar 2019 bisa zanga-zangar neman ‘Rabalushin’ da ya yi jagoranta, wanda daga bisa kotu ta bada belinsa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamna Tambuwal Ya Rusa Shugabannin Riko Na Kananan Hukumomin Jihar Sokoto

Next Post

Allah Ya Yi Wa Iyan Zazzau Da Talban Zazzau Rasuwa

RelatedPosts

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

by Khalid Idris Doya
2 hours ago
0

Kamar dai yadda aka sani kananan hukumomi sune suka kasance...

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Canja Shugabannin Tsaron Nijeriya

’Yan Yankin Arewa Maso Gabas Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Kan Sauke Shugabannin Tsaro

by Khalid Idris Doya
2 hours ago
0

Biyo bayan sauke shugabannin tsaron Nijeriya tare da nada sababbi...

Ya Kashe Mata Da Yaro Da Shebur

by Khalid Idris Doya
3 hours ago
0

A yau aka kama wani mutum mai shekaru 28, Chukwuemeka...

Next Post
Iyan Zazzau

Allah Ya Yi Wa Iyan Zazzau Da Talban Zazzau Rasuwa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version