An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

byCGTN Hausa and Sulaiman
2 weeks ago
Xinjiang

An yi gagarumin bikin murnar cika shekaru 70 da kafa jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kai a birnin Urumqi jiya Alhamis 25 ga watan Satumban nan, inda aka nuna wa duniya manyan nasarorin tarihin da jihar ta samu a cikin shekaru 70 da suka gabata, da kuma tabbatar da fifikon tsarin yankunan mabambantan kabilu masu zaman kansu na kasar Sin, gami da sakamako mai gamsarwa wajen aiwatar da manufofin tafiyar da harkokin Xinjiang da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ke yi a sabon zamani, tare kuma da shaida babbar niyyar da al’ummun jihar Xinjiang ke da ita a fannin raya jiha mai tsarin gurguzu, kuma irin ta zamani, karkashin jagorancin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin.

Kwarewar gwamnatin kasar Sin wajen tafiyar da harkokin mulki, abu ne da yake a bayyane, al’amarin da ya zama babban dalilin da ya kawo manyan sauye-sauye ga jihar ta Xinjiang. Sakamakon matukar kokarin da aka yi, an cimma nasarori da dama wajen dakile ’yan a-ware na wurin, har ta kai ba a samu wakanar ayyukan ta’addanci a tsawon shekaru da dama a yankin ba, al’amarin da ya tabbatar da kwanciyar hankali, da hadin-kan mabambantan kabilun yankin.

Zaman karko shi ne ke haifar da tabbaci ga ci gaban tattalin arziki. Ci gaba mai inganci da jihar Xinjiang ta samu, zai taimaka gaya ga ci gaban sauran kasashe, tare da samar da damarmakin zamanintar da yankin tsakiyar Asiya gami da sauran shiyyoyi.

A halin yanzu, kasar Sin na himmatuwa wajen zamanintar da kanta bisa salon musamman, yayin da aikin zamanintar da jihar Xinjiang ma ke cikin sabon mafari. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kafa alkiblar ci gaban Xinjiang a nan gaba, ciki har da raya sana’o’i na musamman, da bunkasa sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, da raya al’adu da sana’ar yawon shakatawa tare, da inganta aikin kiyayewa, gami da farfado da tsarin muhallin halittu, da gaggauta raya muhimmin yankin tattalin arziki dake kan hanyar siliki da sauransu.

Gagaruman sauye-sauyen da jihar Xinjiang ta samu sun shaida cewa, yadda jama’a ke more rayuwa, hakkin dan Adam ne mafi muhimmanci. Babu shakka, jihar Xinjiang tana fuskantar makoma mai haske. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version