An Shawarci Al’umma Su Rungumi Zumunci A Tsakaninsu
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shawarci Al’umma Su Rungumi Zumunci A Tsakaninsu

byLeadership Hausa
3 years ago
Zumunci

Shugaban kungiyar Zumunta da Taimakon Jama’a, ‘’Community Debelopment Association’’ da ke garin Tafa ta karamar hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, Alhaji Maikudi Dogo, ya yi kira ga al’ummar garin, da kada su sare wajen cigaba da zumunci da zamantakewar da aka san su dashi shekara da shekaru a tsakaninsu.

Shugaban ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake hira da manema labarai yayin gudanar da babban bikinsu na Ajo da suka saba shiryawa akai-akai a harabar ofishin kungiyar da ke garin na Tafa a karshen mako, inda ya yi nuni da cewa, sada zumunci da taimakon juna da al’umma baki daya, sune makasudin kafa kungiyar.

  • Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba
  • “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

Ya kuma ce, yau shekara sama da 20 kenan da suka kafa kungiyar, a lokacin da membobi 60 kacal, amma yanzu, membobin kungiyar sun haura mutum 200 maza da mata da matasa wadanda suka fito daga jihohi daban-daban na fadin kasar nan, yana mai cewa, ” Alhamdu Lillahi, kungiyar cikin shekarun nan, ta tallafa wa membobin ta da dama ta hanyoyi daban-daban, kamar taimako wajen daurin aure, marasa lafiya, jarin yin kasuwanci da sauran su”.

Alhaji Maikudi sai ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da ta waiwaye su, ta taimakawa kungiyar da irin tallafin da take baiwa kungiyoyi a jihar, saboda gagarumin taimakon da take yi wa jama’a musamman marasa galihu, da kuma hobbasar da take yi wajen hada kai da jamai’an tsaro don tabbatar da zaman lafiya a Tafa.

A tasu gudunmawar, mataimakin kungiyar, Alhaji Haladu Musa Usman da kakakin kungiyar (PRO) Alhaji Salisu Hassan, duk kira suka yi ga Gwamnati da ta tallafa wa kungiyar saboda taimakon jama’a da take tayi shekara da shekaru.

Ita ma Shugabar mata, Hajiya Ladidi Kabuga, kira ta yi ga membobin kungiyar, maza da mata, da suci gaba da bin dokokin kungiyar, su kuma zama masu ladabi da biyayya, har ila yau, su kasance masu Kyakkyawar zamantakewa a tsakanin su.

An dai tashi bikin lami lafiya. Cikin manyan bakin da suka halarci bikin akwai Alhaji Danladi Obajana, Alhaji Baffa na ‘yan Canji, Alhaji Musa mai Shadda, Alhaji Abubakar mai DubuDubu, Alhaji Wawan Sarki, Hakimi Uban Badodo daga Bauchi, da Alhaji Dilan fata daga Gombe. Wasu kuma sune, Hajiya Maimuna kawo daga Kano; Hajiya Maryam Oka.

Jamila Gombe; Hajiya Jummai daga Mokwa, da Hajiya Fati Cestelo daga Mararrabar Jos. Sauran sun hada da Usaina daga Mararrabar Jos, Hajiya Bilki daga Kano, da kuma Hajiya Aisha daga Bauchi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Sardaunan Funtuwa Ya Nemi Al’umma Su Tashi Tsaye Wajen Gudanar Da Addu’o’i

Sardaunan Funtuwa Ya Nemi Al'umma Su Tashi Tsaye Wajen Gudanar Da Addu’o'i

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version