Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

An Shiga Rana Ta Biyu Ta Zaman Makokin Mutuwar Maradona

by Muhammad
November 27, 2020
in WASANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abba Ibrahim Wada

An shiga rana ta biyu ta zaman makoki na tsawon kwanaki uku a kasar Argentina domin jimamin mutuwar tsohon tauraron dan kwallon duniya, Diego Maradona wanda ya yi ban-kwana da duniya a ranar Laraba, yana da shekaru 60 sakamakon bugun zuciya.

samndaads

Tuni aka shinfide gawarsa a katafaren ginin Casa Rosada da ke fadar shugaban kasar Argentina domin bai wa jama’a damar ganawa ta karshe ga dan wasan kuma yanzu haka daruruwan mutane sun fara jeruwa a kan layi don ganin gawar tasa daya-bayan-daya.

Tuni aka dage wasa tsakanin Sport Club International da kuma tsohuwar kungiyar Maradona wato Boca Juniors domin karramawa ga marigayin sannan masoyansa sun yi dafifi a filin wasa na Boca Juniors da ke birnin Buenos Aires, inda akasarinsu ke ta rusa kuka shame-shame saboda bakin cikin mutuwarsa.

Maradona ya buga wasa a kungiyoyin kwallon kafa irinsu Barcelona da Napoli, sannan shi ne kyaftin din tawagar Argentina wadda ta lashe kofin duniya a shekarar 1986, inda a wancan lokacin aka zarge shi da yin amfani da hannu wajen jefa kwallo a ragar Ingila a matakin kwata fainal na gasar.

Maradona ya mutu ne makwanni da yi masa tiyata a cikin kokon kansa sakamakon daskarewar jini a kwakwaluwarsa, sannan ya yi fama da masifar kwankwadon barasa da hodar ibilis kodayake mai shigar da kara na gwamnatin Argentina ya ce, za a gudanar da gwajin kan gawarsa.

Tuni tsoffin ‘yan wasa har ma da wanda ke kan ganiyarsu suka fara aikewa da sakon ta’aziyar rashin Maradona, inda Pele da ake kallo a matsayin babban abokin hamayyarsa ya ce, yana fatan za su hadu wata rana a lahira domin buga wasa.

SendShareTweetShare
Previous Post

NIS Ta Yi Bankwana Da Daya Daga Cikin Manyan Jami’anta Da Ya Yi Ritaya

Next Post

FIFA Ta Fitar Da Sunayen Da Za A Zabi Gwarazan Shekara A Matakai

RelatedPosts

Lukaku

Za Mu Iya Lashe Gasar Siriya A – Lukaku

by Sulaiman Ibrahim
21 hours ago
0

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Inter Milan,...

Pogba

Mun Shirya Doke Liverpool, Cewar Pogba

by Sulaiman Ibrahim
21 hours ago
0

Dan wasan tsakiyar kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, Paul...

Mourinho

Mourinho Ya Caccaki ‘Yan Wasansa

by Sulaiman Ibrahim
21 hours ago
0

Kociyan kungiyar Tottenham, Jose Mourinho ya koka da rashin kokarin...

Next Post

FIFA Ta Fitar Da Sunayen Da Za A Zabi Gwarazan Shekara A Matakai

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version