Abdullahi Sheme">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Yaba Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Kasa INEC

by Abdullahi Sheme
December 20, 2020
in LABARAI
2 min read
INEC
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

An yaba ma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC, yabon ya fito ne daga bakin Birgediya Janar Maharazu Isma’il Tsiga mai ritaya Basarake, manomi, dan siyasa shi ne Barden Kudun Katsina a fadarshi dake garin Tsiga a karamar hukumar Bakori dake jihar Katsina.

Barden Kudun Katsina ya yi hira da manema labarai a makon da ya gabata jim kadan da kada kuri’arshi a zaben cike gurbi na dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Bakori a majalisar dokoki ta jihar Katsina a sanadiyyar rasuwar dan majalisar jihar.

samndaads

Birgediya janar ya cigaba da cewar babu shakka ya gamsu kwarai akan yadda yaga shirin hukumar zaben yadda suka samar da kayan zabe gamsassu da kai kayan zabe cikin lokaci da bude rumfunan zabe cikin lokaci da na’urar tantance masu jefa kuri’a, wannan ya nuna hukumar zabe ba irin wadda aka sani a shekarun baya bace domin duk abinda masu jefa kuri’a suke nema wadda doka ta tanadar hukumar zabe ta kawo kuma babu shakka mutane sun fito wajen zaben kuma anyi zabe lafiya domin babu inda aka sami tashin hankali ko wani yamutsi.

Daganan yayi kira ga masu jefa kuri’a su kara rike ‘yancin su domin kuria ce yancin su, kuma su ma al’umma sun fara ganewa domin sun san kuriar itace yancin su.

Alhaji Maharazu Tsiga wanda ya taba neman kujerar dan majalisar dattawa a mazabar  shiyyar Funtuwa a jam’iyyar APC wanda ya kara kira ga duk wanda bai samu nasara ba da yayi hakuri domin mulki na Allah ne shi ke badawa kuma komai lokaci gareshi don haka don Allah wanda duk ya samu nasara ya gode ma Allah kuma wanda ya samu kada ya dauka kamar ya fi kowa ne, shi kuma wanda bai samu ba kada ya dauka ko Allah baya sonshi ne, wannan ba haka bane, yace yanzu ina wanda ya fara cin zaben Allah yayi mashi rasuwa da fatan Allah  ya jikanshi, Barden kudun Katsina yace duk dan siyasar dake son ya koyi hakuri yazo wurinshi don yasan komai na Allah ne.

Shi dai Alhaji Maharazu Tsiga yana na farko farkon da ya fito neman kujerar sanatan yankin Funtuwa a Jam’iyyar APC amma bai samu ba kuma yayi hakuri inda yake zaune a garinsu cikin Al’ummarshi inda yake taimakon jama’ar yankin su, wakilinmu ya gano yadda jama’ar garin ke yaba mashi da yayi ritayar aikin soja ya dawo gida yake taimakon Al’umma a lokaicn da yake aikin soja ya taimaki matasan yankin da samun ayyukan gwamnatin tarayya da samar ma matasan yankin da sauran Al’umma tallafi daban daban.

SendShareTweetShare
Previous Post

Dan Majalisar Wakilai Alhaji Muktar Dandutse Ya Horas Da Matasa Dabarun Noman Shinkafa Na Zamani A Mazabarsa

Next Post

ICAN Ta Gudanar Da Taronta Karo Na Sha Biyar A Kano

RelatedPosts

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

by Abdullahi Sheme
10 hours ago
0

Daga Abba Ibrahim Gwale, Shugaban kasa Muhammad Buhari ya amince...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yau Za A Yi Karon Batta A Zaben Kananan Hukumomin Jihar Kano

by Abdullahi Sheme
20 hours ago
0

 Jam’iyyu 11 ne za su fafata PDP Kwankwasiyya ta ce,...

Sojoji

Tsofaffin Sojoji Sun Nemi Karin Kudin Fansho

by Abdullahi Sheme
20 hours ago
0

Kungiyar tsofaffin sojoji ta kasa reshen jihar Anambra ta bukaci...

Next Post
ICAN

ICAN Ta Gudanar Da Taronta Karo Na Sha Biyar A Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version