Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

An Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Samar Da Cibiyoyin Warkar Da ‘Yan Kwaya

by Muhammad
April 6, 2021
in RAHOTANNI
3 min read
An Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Samar Da Cibiyoyin Warkar Da ‘Yan Kwaya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba,

An yaba wa kokarin da gwamnatin jihar Kaduna ke kan  yi na samar da cibiyoyi hudu na warkar da masu tu’amalli da kayan maye a jihar.

Yabon ya fito ne daga bakin Shugabar Gidauniyar  tallafa wa Mata da Matasa da ake kira a turance Eye Opener Women &  Youth Foundation,  Uwargida  Magret Juliu.

Uwargida  Magret Juliu ta kuma yi nuni da cewa, , Cibiyoyin za su taimaka matuka wajen dai daita rayuwar su da kuma  samar masu da lafiya.

Shugabar Magret Julius ta sanar da hakan ne   a kaduna a  hirar ta kamfanin dillancin labarai na kasa,  inda ta yi nuni da cewa,  lamarin abin damuwa ne matuka.

Magret Julius ta yi nuni da cewa,  lamarin abin damuwa ne matuka.Ta kuma koka kan yadda wasu mata da matasa ke yin tu’amalli da kayan maye.

A cewar Uwargida  Magret Julius,  tsamo matan da matasan da suka cusa kansu a cikin harka  ta shan kayan maye,  abu ne da ke bukatar sa hannun ‘yan uwa da kuma alummar gari.

Shugabar Uwargida  Magret Julius ta ci gaba da cewa,  “Gidauniyar mu na kan gudanar da aiki kafada da kafada da ‘yan uwan irin wadanan masu yin tu’amalli da kayan maye kan yadda za a tsamo su daga cikin mummnar dabi’ar,  inda ta yi nuni da cewa,  akwai kuma bukatar ‘yan uwan  masu  yin irin wannan dabi’ar su dinga nuna maau so da kauna ba tare da nuna masu kyama ba”.

Uwargida  Magret Julius ta kara da cewa, “ Gidauniyar  na bayar da shawara da kuma janyo ‘yan uwa da shugabannin alumma da kuma masu ruwa da tsaki domin wayar da kai  kan yadda za su kula da irin wadannan masu dabi’ar da suka tsuduma a cikin matsala sanadiyyar yin tu’amalli da kayan maye.

Ta kara da cewa , “Idan  matsalar ta kama mutum daya,  kamar ta shafi daukacin ‘yan uwa ne da kuma daukacin alumma,  inda ta bayyana cewa,  hakan ne ya sa muka zage tukuru,  wajen yin fadakar wa kan illolin dake tattare da yin tu’amalli da kayan maye  da kuma irin matsalar da dabi’ar ke haifar wa masu yin ta.

Ta ce, Gidauniyar ta kuma gudanar da tarurtuka da ban da ban kan yadda ‘yan uwa za su taimaka wa masu tu’amalli da kayan maye da suka  samu wasu larurori domin su samu sauki su kuma koma cikin alummma su ci gaba da rayuwa ta gari.

Uwargida  Magret Julius ta yaba wa Gwamatin Tarayya da kuma Gwamnatin jihar Kaduna kan kokarin da suke ci gaba da yi na yakar shan kayan maye.

Ta karada cewa,  Gidauniyar ta yi hadaka da Hukumar yaki da sha da safafar kayan maye  NDLEA da kuma Hukumar yaki da sha kayan maye mallakar gwamnatin  jihar   KSBDSA domin tabbatar da Yaki da shan kayan maye a daukacin fadin  jihar.

Uwargida  Magret Julius,  Gidauniyar na kuma dora mutane kan yadda za su koyi sana’oin hannu,  musamamn a tsakanin mata da matasa,  inda ta kara da cewa ,  Gidauniyar ta kuma horar da  sama da mata da matasa 1,000 kan sana’oin hannu da ban da ban da suka hada da yin Takalma,  Jakankuna, aikin Tela da sauransu.

Uwargida  Magret Julius ta sanar da cewa,  horon an bayar dashi ne ta hanyar  sauran kungiyoyi masu ra’ayi daya kuma Gidauniyar ta rabar da kyautar ‘ykn kudade ga  wadanda suka amfana da horon domin su fara gudanar da kasuwanci don su zamo masu dogaro da kawunan su,  inda ta  yi kira ga matasa da su yi watsi da yin tu’ammali da kayan maye, musamamn domin kare lafiyarsu da kuma ganin cewa,  sune manyan gobe.

SendShareTweetShare
Previous Post

Za Mu Yi Saukar Alkur’ani 1,111 Domin Zaman Lafiya A Kasa – Gwani Aliyu Turaki

Next Post

Za Mu Yi Kaca-kaca Da ‘Yan Ta’adda Nan Ba Da Jimawa Ba – Sojin Sama

RelatedPosts

Amin

Yadda Ta Kaya A Taron Tunawa Da Malam Aminu Kano Karo Na 19

by Muhammad
20 mins ago
0

Mun Gamsu Da Yadda Aka Tsara Taron Kan Tsaro Da...

AKCOE

Mataimakin Shugaba Kwalejin AKCOE Ya Zama Jakadan Zaman Lafiya A Nijeriya

by Muhammad
45 mins ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, Mataimakin Shugaban Kwalijin Ilimi ta Aminu Kano...

Allah

An Roki Al’umma Su Dogara Ga Allah  

by Muhammad
1 hour ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Alhaji Bello Otunba wanda yake daya...

Next Post
Za Mu Yi Kaca-kaca Da ‘Yan Ta’adda Nan Ba Da Jimawa Ba – Sojin Sama

Za Mu Yi Kaca-kaca Da 'Yan Ta'adda Nan Ba Da Jimawa Ba - Sojin Sama

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version