Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Yaba Wa TAJBank A Kokarinsa Na Bunkasa Bangaren Ilimi

by Muhammad
January 11, 2021
in LABARAI
2 min read
TAJBank
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mahdi M. Muhammad,

 

samndaads

Bankin TAJBank wanda ake ganin a yanzu ya fi kowane Banki kirkiro sabbin abubuwan cigaba a Nijeriya, ya sake jaddada kudurinsa na bada gudumawa ga ci gaba da bunkasa bangaren ilimi a duk fadin Nijeriya.

Wannan ya fito fili ne a yayin kaddamar da sabbin kayan aiki a makarantar ‘Saint John Paul’, da ke jihar Akwa Ibom, tare da manyan mutane da dama da suka halarci taron, kamar su Sanata Godswill Akpabio, Ministan harkokin Neja-Delta, Shugabar makarantar, misis Uloma Akpabio, Mai gudanarwa na NDDC, Akwa Efiong da sauran manyan baki.

Sanata Akpabio ya kuma bukaci Bankin da ya bude reshe a Uyo a matsayin fifiko da zarar ya samu lasisin sa na kasa.

Wanda ya wakilci Bankin a wannan taron, Mista Nasir .T. Usman ya yarda da gagarumin ci gaban da shugabancin makarantar ‘Saint John Paul’ na Akwa Ibom ya yi don cike gibin ilimi mai inganci a Nijeriya ta hanyar la’akari da muhimman abubuwan da suka shafi fahimtar irin wannan bukatar ta wadatar jama’a. Ya kuma ce, sakamakon ya kasance bayyananne a cikin shekaru tara na makarantar, kasancewar ta yi nasarar kirkirar dalibai hazikai masu hazakar ilimi da matsayi mai kyau.

Ya ci gaba da bayyana cewa a cikin sama da shekara guda na fara aiki, TAJBank ya yi nasara a manyan lamura da dama. ya ce, Kwanan nan Kamfanin Jaridar LEADERSHIP ya ba Bankin lambar girmamawa a matsayin Bankin Shekarar 2020, bisa la’akari da kwazon sa da kokarin sa na shigar da kudi ga mutane daga tushe.

Ya ce, TAJBank yana ba da samfuran ayyukan hulda ga abokan cinikinsa. Wasu daga cikin wadannan kayayyakin sun hada da, Abokin Hulda (Mudarabah) Adadin Lokaci, Hayar (Ijarah) Kudi, Abokin Hulda (Mudarabah) Ajiye ko kuma Asusun Yanzu, da dai sauran su.

Bugu da kari, TAJBank shi ne Banki na biyu a Nijeriya da ke ba da bashi ba tare da ruwa ba. Bankin ya sami lasisi daga Babban bankin Nijeriya a ranar 12 ga watan Yulin 2019. Haka zalika, Bankin yana ba da kaya da ayyuka masu ban sha’awa, wadanda suka hada da Bankin kamfanoni masu zaman kansu, Kasuwancin banki, bankin Kasuwanci, raya ayyuka ci gaba da na jama’a.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sanata Na’Allah Ya Bukaci NLC Ta Hada Kai Da Gwamnati A Kebbi

Next Post

Mummunan Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 20 A Bauchi

RelatedPosts

Jami’an NIS Na Samun Horo A Kan Amfani Da Dokokin Shige Da Ficen ƙasa

Jami’an NIS Na Samun Horo A Kan Amfani Da Dokokin Shige Da Ficen ƙasa

by Sulaiman Ibrahim
7 hours ago
0

Shirin yaƙi da safarar bil’adama da fasa-ƙwaurin ‘yan gudun hijira...

‘Yan Nijeriya Mutum Miliyan 15 Na Shan Kwayoyi, Inji Buba Marwa

‘Yan Nijeriya Mutum Miliyan 15 Na Shan Kwayoyi, Inji Buba Marwa

by Muhammad
9 hours ago
0

Shugaban Hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun...

Katin Zama Dan Kasa

Nijeriya Ta Wajabta Wa Jami’an Diflomasiyya Mallakar NIN

by Sulaiman Ibrahim
16 hours ago
0

A jiya Lahadi Gwamnatin Tarayya ta shaida cewar, ya zama...

Next Post
Mummunan

Mummunan Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 20 A Bauchi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version