Yusuf Abdullahi Yakasai">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Yi Babban Taron Zaman Lafiya Da Hadin Kai Tsakanin Mafarauta A Legas

by Yusuf Abdullahi Yakasai
February 12, 2021
in LABARAI
1 min read
An Yi Babban Taron Zaman Lafiya Da Hadin Kai Tsakanin Mafarauta A Legas

Exif_JPEG_420

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Marafauta na jihohin Yamma sun gabatar da taro a yankin Abatuwa da ke Legas.

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban mafarauta na Legas Olu Ogunronbi, ya nuna farin cikinsa ga wannan taro ya kuma roki jama’a a hada kai a zauna lafiya. “Mu marafauta kanmu a hade yake mun kiyaye duk abin da muka sa gaba Allah ya sa mu samu daurewa, shugaban mafarauta na yankin Legas ya kara da cewa kowa ya tabbatar mai farauta ya mallaki katin shaida, motocin zuwa farauta su tabbatar sun sa shaida a gaban motarsu domin kowa ya sani.
Saboda haka ya gode wa shugabannin Arewa da suka hada wannan taro.
Shi kuma a nasa jawabin, sarkin dawa na Arewa da ke Legas Alhaji Kabiru Ori ya yi farin ciki da ganin shugabanni daban-daban su ka zo wannan taro, kuma Sarki Kabiru ya kara cewa a shirye dokokin da aka shinfida kuma za su ci gaba da tattaunawa da jama’arsa, saboda haka ya gode, Allah ya mai da kowa gi da lafiya.
Shi kuma a nasa jawabin Alhaji Ado Shu’aibu Dansodo daya daga cikin manyan shugabanni a Legas ya yi farin ciki da wannan taro ya kuma nemi a zauna lafiya. Kabiru ya kara da cewa tsakanin mafarautan Arewa da abokanan zamansu na yamma akwai kyakkyawar fahimtar juna.
Shi kuma a nasa jawabin, mai masaukin baki Alhaji Danjuma Abatuwa Lagos ya yi godiya da wannan taro inda ya bayyana cewa ya ji dadi an zo lafiya an kuma tashi lafiya.
Daga cikin mutanan da suka zo akwai Olu Ogunronbi Abinbun, Aguniyi Babagun, Rasaki Shoetan, Akintunde Haruna, Ganiyu Aladajo. Sauran su ne: Abubakar Mogaji, Alhaji Ado Shuaibu, Kahlid Chitansi, Danlifi Baban Rabi Kaura Gezawa da kuma Alhaji Sani Wambai.

SendShareTweetShare
Previous Post

Al’ummar Musulmi Ta Halarci Addu’ar Kwana 40 Na Marigayi Iyan Zazzau

Next Post

‘Yan Arewa Mazauna Legas Mu Fito Don Gyara Rajistar Katin Zabe – Alhaji Sa’adu Gulma

RelatedPosts

Garkuwa

An Kama Sojan Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Kayan Sojoji A Zamfara

by Yusuf Abdullahi Yakasai
2 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim "An kama wani jami’in soja da budurwarsa...

Aikin Wutar Mambilla  A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

Aikin Wutar Mambilla A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

by Yusuf Abdullahi Yakasai
5 hours ago
0

Kungiyar gwamnonin arewa maso gabas sun nuna rashin jin dadin...

Bindiga

Gwamna Ortom Ya Yabawa Umarnin Buhari Na Hana Mallakar  AK47 Ba Bisa Ka’ida Ba

by Yusuf Abdullahi Yakasai
7 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Gwamnan Jihar Benue Samuel Ortom a ranar...

Next Post
‘Yan Arewa Mazauna Legas Mu Fito Don Gyara Rajistar Katin Zabe – Alhaji Sa’adu Gulma

‘Yan Arewa Mazauna Legas Mu Fito Don Gyara Rajistar Katin Zabe – Alhaji Sa’adu Gulma

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version