Mustapha Abdullahi">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Yi Kira Ga El-Rufa’i Ya Gargadi Masu Kokarin Rushe Tashoshin Mota

by Mustapha Abdullahi
January 30, 2021
in LABARAI
2 min read
An Yi Kira Ga El-Rufa’i Ya Gargadi Masu Kokarin Rushe Tashoshin Mota
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban kungiyar Direbobi ta kasa NURTW reshen Jihar Kaduna, Alhaji Aliyu Tanimu Zariya ya yi kira ga Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufa’i da ya gargadi hukumar kula da gine-gine ta Jihar da ke rushe tashar mota, ba tare da yi wa dimbin jama’a tanadin wurin da za su zauna domin ci gaba da sana’o’insu ba.

Alhaji Aliyu Tanimu Zariya, ya yi wannan kiran ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a ofishinsa da ke Kaduna.

Shugaban NURTW reshen jihar Kaduna ya shaida wa manema labarai cewa su a kodayaushe masu yin biyayya ne ga Gwamnati, don haka suke bayar da shawarar cewa idan za a rushe Tashar mota, to a yi kokarin sama wa dimbin ‘ya’yan kungiyar da ke neman abin da za su ci tare da iyalansu wurin da za su koma domin ci gaba da sana’arsu.

“An rushe tashar Unguwar Talbishin da ake kira talbishin/ Kakuri, bayan an rushe sai aka ce masu su koma KSTA, amma kuma wanann wuri ba gyara, ba wutar lantarki, ba ruwa, ba tsaro, saboda haka ta yaya jama’a za su kai dukiyarsu a wannan wuri. Ko su ‘ya’yan kungiyarsu su koma domin ci gaba da gudanar da sana’arsu a wurin,” ya tambaya.

Alhaji Aliyu Tanimu Zariya ya kuma bayyana goyon bayansa ga Gwamnatin Jihar, wanda dalilin hakan ne ma ya sa suke kokarin sayar da rasidin gwamnati a dukkan tashoshin motocin da yake suna gudanar da sana’arsu ta tuki tsawon shekaru da dama.

Ya ce, “muna kuma maraba da shirin Gwamnati na kokarin duba lafiyar direbobi idan lokacin hakan ya zo, amma muna jiran umurnin uwar kungiya ta kasa a kan wannan batu.”

SendShareTweetShare
Previous Post

Abin Da Ya Sa Muke Kula Da Rasidi -Shehu Bello

Next Post

NAF Ba Ta Sassauta Wa ‘Yan Ta’addan Nijeriya Ba – Shugaban Sojin Saman Nijar

RelatedPosts

‘Yan Gudun Hijira Na Fuskantar Matsalar Abinci A Sansanin Jalingo

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 60, Tare Da Kone Kauye A Zamfara

by Mustapha Abdullahi
5 hours ago
0

Al'ummar garin Ruwan Tofa a karamar hukumar Maru ta jihar...

Rigakafin Korona

Rigakafin Korona: Yau Gwamnoni Za Su Yi Kus-kus

by Mustapha Abdullahi
12 hours ago
0

Daga Nasir S. Gwangwazo, Abuja   A yau Alhamis, 4...

Borno

Akwai Bukatar Nijeriya Ta Nemo Sojojin Haya Don Yakar ‘Yan Ta’adda – Zulum

by Mustapha Abdullahi
12 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Bauchi   An bai wa Gwamnatin...

Next Post
NAF Ba Ta Sassauta Wa ‘Yan Ta’addan Nijeriya Ba – Shugaban Sojin Saman Nijar

NAF Ba Ta Sassauta Wa ‘Yan Ta'addan Nijeriya Ba – Shugaban Sojin Saman Nijar

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version