An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

byRabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Taraba

Wasu da ba a san ko su waye ba sun yi wa wata yarinya ‘yar shekara 18 mai suna Miss Wassa Joel Tuwa ‘yar Karamar Hukumar Yoro ta jihar Taraba fyade har lahira a hanyar wani daji da ke kauyen Rankabiri kusa da Jalingo babban birnin Jihar Taraba.

Wata majiyar daga dangin wacca abin ya shafa, Mista Ayuba Solomon Bissa ya shaida wa wakilinmu cewa an yi wa Mis Tuwa fyade tare da kashe ta yayin da aka jefa gawar a bayan wani dutse kusa da Jalingo.

  • Wasu Hukumomin Kasar Sin Sun Ware Miliyoyin Kudi Domin Tallafawa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa
  • Rikicin Nijar: Tinubu Ya Aika Janar Abdulsalami, Sultan Na Sokoto Zuwa Yamai

A cewar Ayuba, marigayiyar ta bar gidansu da ke Jalingo zuwa Lankabirir, wani kauye kusa da yammacin ranar Asabar. Ta bi ta wata karamar hanyar kasuwa da ke kusa da Lankabiri don ta samu saukin tafiyar inda a nan ne suka tare suka yi mata fyade har ta mutu.

Ya kuma bayyana cewa binciken da likitocin suka gudanar ya nuna cewa an yi wa matar fyaden ne kafin daga bisani a kashe ta.

“A ranar Lahadi da safe ne wani karamin yaro da ke tallan itace ya gano gawar ta a gefen hanya, ya koma a guje ya sanar da iyayensa abin da ya gani, sai iyayen yaron da sauran mazauna wurin suka je wurin, suka gano gawarta a gefen hanya kusa da wani dutse.

“Ba mu taba gawarta ba, amma dai mun gayyaci jami’an tsaro da ke aiki a yankin domin su gani da kuma ba da shawara kan abin da za a yi, jami’an tsaron da suka hada da sojoji da ’yan sanda sun zo suka ba mu shawarar da mu kai gawar zuwa dakin ajiyar gawarwaki, mu ba da damar yin bincike.

“Mun kai gawar zuwa cibiyar kula da lafiya ta tarayya Jalingo bayan likitan da likita ya kammala gudanar da bincike ya tabbatar mana da cewa an yi mata fyade ne kafin a daga baya a kashe ta.

“Ina so in yi kira ga jami’an tsaro da su zurfafa bincike domin a gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban kuliya,” in ji Ayuba.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Jihar Taraba, PPRO Usman Abubakar, ya ce har yanzu rundunar ba ta samu cikakken bayani kan lamarin ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari Wani Coci A Osun

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari Wani Coci A Osun

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version