Sani Hamisu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RIGAR 'YANCI

An Yi Zanga-Zangar Salon Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa A Najeriya

by Sani Hamisu
July 2, 2019
in RIGAR 'YANCI
3 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gamayyar kungiyoyin fararen hula a Abuja, sun koka kan yadda gwamnatin tarayya ke kauda ido aka hukunta wasu jami’anta da ake zargin da cin hanci, lamarin da ke haddasa kokonto kan yaki da cin hanci da ake yi a kasar. Kungiyoyin kare hakin jama’ar sun gudanar da zanga-zanga da zaman dirshan na wasu sao’i a Abuja, bisa abin da suka bayyana damuwarsu kan rashin daukan matakin da shugaban kasar ke yi a kan batutuwa na cin hanci da rashawa da suke ganin lamarin na wuce gona da iri.

Su dai masu wannan zanga-zangar sun gudanar da wani zaman dirshan a dandalin yanci da ke Abuja, akan batutuwan da suka danganta da rashin daukar matakai da gwamnatin kasar taki yi akan masu cin hanci da rashawa da ake yi wa jami’an gwamnatin Najeriya.

Kama daga kan sakataren gwamnatin kasar da aka dakatar da shi bisa zargin almundahana, ta Naira Milyan Dari biyu da tsaba’in, wanda duk da mika rahoto ga bangaren gwamnatin amma shiru kake ji izuwa ga batun shugaban hukumar leken asiri, da shima aka gano tsabar kudi har Dala miliyan hamtsin shima din shiru kake ji kamar an shuka dusa.

Ga na baya-bayan nan na kamfanin NNPC na man fetur din Najeriya, da suka ce ta kai ga nuna wa juna yatsa tsakanin sa da Ministan kasar a ma’aikatar man, da   shugaban kamfanin na NNPC, sannu a hankali sun ce ana neman mai da batutuwan na zargi-zargen cin hanci da ke faruwa a karkashin gwamnatin shugaban Muhammadu Buhari wanda lamarin na neman zama wasan yara don haka baza su lamunta ba.

Commared Bako Abdul Hassan, shine shugaban kungiyar Campaign for Democracy, wanda yake Kaduna, yace “mun gaji da gafara sa bamu ga kaho ba, yau akwai abubuwan da suke faruwa game da tafiyan shugaban cin kasar nan, Janaral Muhammadu Buhari shugaban mu lokacin da ya hau mulki mun ga kowa ya nutsu, kowa ya dawo taitayin shi.”

“Amma daga baya mutanen da ya dauka suna aiki a tare da shi kamar Sakataren gwamnati almundahana na kudin jama’a da suka yi a NNPC, an dawo an zargi shi shugaban ‘yan sanda dan wannan abun zai shafi mutumcin shi mun san shi bame almundahana bane da dukiyan jama’a, to idan yasan bazai iya ba to ya yada kwallon mangoro ya huta.”

Masu zanga-zangar sun yi alkawarin ci gaba da zanga-zangar hade da zaman dishan har sai Baba ta gani a kowacce rana a dandalin yanci da ke Abuja. To amma basa ganin abubuwane da ake bincike akan su sannu a hankali. Commared  Deji Adeyanju, jigo ne a kungiyar masu fafutuka akan wannan lamari ya ce.

“Maganganu da Ministan NNPC yayi wannan maganganun ne yasa hankalin mu ya tashi muka ce la irin wannan kudin mutum guda daya ne yazo ya bada kwangila, ba wanda ya sani, daga baya shekaran jiya muka ji Presidency suka fito suka ce ba wani magana, miliyan ashirin da biyar wai babu wannan  maganan haka.

“Sai mu ka ce indai babu maganar haka to ya kamata Buhari ya sauke shi daga matsayin sa na Minista , to abubuwan nan bai faru ba har zuwa yanzu da nake wannan maganar, mun fitone domin shugaban kasar mu ya dauki mataki akan wannan maganganun tun shekarar da ya wuce har akan Babati Lawan, babu wani mataki da aka dauka saboda shugaban kasa ya rufe kunnen shi. Wannan ba daidai bane wannan abun ya koma kamar rainin hankali.”

Abin jira a gani shine ko zanga-zangar da zaman dirshan irin wannan zai samu dorewa dama yin tasiri  na samun sauyi daga bangaren gwamnatin. Domin ta hanzarta fitar da sakamakon rahotanni na bincike-binciken da aka gudanar akan zargin cewa jami’an da ke aiki a karkashin ta sun aikata ba daidai ba, a amanar da aka mika musu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Jigawa Ta Amince Da Dokar Manyan Laifuka

Next Post

Barkewar Sabon Rikici A Binuwe Ya Ci Rayukan Mutum 12

RelatedPosts

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by Sani Hamisu
1 week ago
0

Daga Abdullahi Muh’d, Kano Shugaban Gidauniyar ‘Charity’ mai rajin tallafa...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by Sani Hamisu
1 week ago
0

Daga Zubairu M Lawal, A yayin da uwar jam'iyyar APC...

Shafukan

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by Sani Hamisu
1 week ago
0

Daga Umar Faruk, Gwamnan Jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu, a...

Next Post
‘Yan Jagaliyar Siyasa Sun Farmaki Matar Atiku Abubakar

Barkewar Sabon Rikici A Binuwe Ya Ci Rayukan Mutum 12

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version