Ancelotti Zai Zama Kociyan Tawagar Brazil A 2024
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ancelotti Zai Zama Kociyan Tawagar Brazil A 2024

byAbba Ibrahim Wada
2 years ago
Brazil

Mai koyar da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid Carlo Ancelotti ya amince da karbar ragamar horar da tawagar ‘yan wasan kasar Brazil a shekara ta 2024, in ji shugaban hukumar kwallon kafa ta kasar, Ednaldo Rodrigues.

Brazil, wadda ta lashe gasar cin kofin duniya sau biyar ta yi amannar cewa dan kasar Italiyan shi ne ya fi dacewa da ya kai Brazil Copa America da za a yi a watan Yunin 2024.

  • Kiwon Lafiya: Yadda Dabi’un Ko-in-kula Ke Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
  • Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Rodrigues ya ce mai koyarwa Fernando Diniz zai ci gaba da lura da kungiyar ta Brazil da ake kira Selacao tare da ci gaba da aikinsa na horar da Flumine har zuwa lokacin da Ancelotti zai karbi aiki wato idan kwantiraginsa ya kare da Real Madrid.

“Shi ne zai mika wa Ancelotti ragamar Brazil kuma salon wasansa ya yi kusa da na kocin da zai karbi aikin kai kungiyar gasar cin kofin Copa America, wato mista Ancelotti” in ji Rodrigues.

Ya ci gaba da cewa ba za su kira shi kocin rikon kwarya ba ga tawagarsu ta kasa,

Brazil dai ta kasance ba ta da mai koyarwa tun bayan kammala gasar kofin duniya da aka kammala a bara, lokacin da Tite ya ajiye aiki bayan cire kasar da Croatia ta yi a wasan kusa da daf da na karshe.

Kocin da ke jan ragamar tawagar ‘yan kasa da shekara 20 ne ke lura da Brazil a wasanni sa da zumunta da take yi a kwanakin nan kuma Ancelotti mai shekara 64 ya koma Real Madrid ne a shekarar 2021 bayan ya bar Eberton, kuma tun bayan komarwarsa ya ci Champions da La Liga da Copa del Rey da sauransu.

Da kofin zakarun Turai da ya lashe a 2022 a wasan karshe a hannun Liberpool, Ancelotti ya lashe kofin nahiyar Turai na hudu kenan a matsayinsa na koci, na biyu a Real Madrid bayan biyu da ya lashe a AC Milan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version