APC Da NNPP Sun Lashe Zaɓen Cike Gurbi Na Majalisar Dokokin Kano
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Da NNPP Sun Lashe Zaɓen Cike Gurbi Na Majalisar Dokokin Kano

bySulaiman
2 months ago
NNPP

Jam’iyyar NNPP da APC sun samu nasara a zaɓen cike gurbi na jihar Kano da aka gudanar a ranar Asabar.

 

Da yake sanar da sakamakon da misalin karfe 12:36 na daren Lahadi, Jami’in zaɓe na hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC), mai kula da mazaɓar Bagwai/Shanono, Farfesa Hassan Adamu Shitu, ya bayyana dan takarar jam’iyyar NNPP, Dr. Ali Hassan Kiyawa a matsayin wanda ya lashe zaɓen da kuri’u 16,198 kan Ahmad Muhammad Kadamu na APC, wanda ya samu kuri’u 5,347.

  • Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?
  • Zaɓen Cike Gurbi: Jauro APC Ne Ya Lashe Kujerar Ganye Ta Adamawa – INEC

Har ila yau, da misalin karfe 6:10 na safiyar Lahadi, jami’in zaɓe na INEC mai wakiltar Ghari/Tsanyawa, Farfesa Muhammad Waziri, ya bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Garba Ya’u Gwarmai a matsayin wanda ya lashe zaɓen da kuri’u 31,472 inda ya doke Yusuf Ali Maigado na NNPP, wanda ya samu kuri’u 27,931.

 

An gudanar da zaɓen ne bayan da INEC ta ayyana zaɓen a baya a matsayin wanda bai kammalu ba.

 

LEADERSHIP ta ruwaito a ranar Asabar cewa, jam’iyyar APC ta yi watsi da yadda zaɓen ya gudana, inda ta bukaci a soke zaɓukan biyu bisa zargin tayar da tarzoma daga ayyukan ‘yan daba.

 

Kiran ya sa shugabannin NNPP suka gudanar da zaman dirshan a ofishin tattara sakamakon zaɓen, inda suka zargi hukumar da yunkurin yin magudi a mazaɓar Ghari/Tsanyawa.

 

Mai magana da yawun gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa wanda ke cikin shugabannin NNPP, ya tabbatar da cewa ‘ya’yan jam’iyyar ba za su fice daga cibiyar tattara sakamakon zaɓen ba har sai an bayyana sakamakon a hukumance.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Tattakin Arba’in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

Tattakin Arba'in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version