Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

APC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki a Kebbi

by Tayo Adelaja
September 26, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk, Birnin-Kebbi

Jam’iyyar APC a Jihar Kebbi ta gudanar da taron masu Ruwa da tsaki na jihar a jiya, a dakin taro na masaukin shugaban kasa da ke Birnin-kebbi.

samndaads

Taron dai ya samu halartar manyan  masu Ruwa da tsaki na jihar ta kebbi da manyan Ma’aikatan gwamnatin , sun hada da Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, maitamakin kakakin majilasar dokoki ta Jihar, memba Muhammad Buhari Aliero, Ambassada Isah Muhammad Argungu, Shugaban Jam’iyyar APC ta jihar kebbi, Barista Attahiru Maccido, mataimakan shugaban jam’iyyar APC na yankuna uku na jihar da kuma membobin majalisar dokoki ta jihar kebbi.

Sauran sun hada da shugaban jam’iyyar APC na kananan hukumomi 21, Shugabanin kananan hukumomin mulki a jihar, Sakataren Gwamnatin jihar ta kebbi Babale Umar Yauri, Shugaban Ma’aikatan gidan Gwamnatin Suleiman Muhammad Argungu, da kuma Mai bada shawara ga Gwamna kan harakokin Siyasa,Yusufu Haruna.

A jawabin da shugaban jam’iyyar APC na jihar, Barista Attahiru Maccido ya gabatar a wurin taron ya bayyana cewa uwar jam’iyya ta kasa ita ce ta gudanar da wani taro irin wannan da manufar duba kiraye- kirayen da wasu bangarorin nan kasar ke yi, inda  ta kafa kwamiti na wasu Gwamnomin da wasu manyan ‘yan jam’iyyar ta APC,  domin binciken ra’ayin kowanne yankin kasar nan kan sake gyaran fasalin kasa. Kan wasu tsare-tsare na tafiyar da mulkin kasar nan.

Har ila yau, ya ce saboda hakan ne aka aike wa da kowacce jiha da jam’iyyar APC ke mulki takardar umurnin gudanar da taron masu ruwa  da tsaki domin fito da shawarwarin yadda za a shawo kan wannan kiraye-kirayen da ake ta ci gaba da yi, inda  za a duba halin gyaran ko rashin yi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Makiya Ne Ke Son Ganin Bayana –Tanimu Sada

Next Post

Trump: Jaba Tsoma Baki A Bar Mi Ki

RelatedPosts

Kwazon Tambuwal

Hobbasar Kwazon Tambuwal Na Fara Biyan Albashi Daga Haraji A 2023

by Muhammad
3 hours ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Gwamnatin Jihar Sakkwato a karkashin jagorancin...

Alan Waka

Aminu Alan Waka Ya Yi Bayani Game Da Sarautar Danburan Din Gobir

by Muhammad
3 hours ago
0

Daga Mukhtar Yakubu, A farkon shekarar nan ne ta 2021...

Jami'ar Bayero

Cibiyar Nazarin Dimokradiyya Ta Jami’ar Bayero Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Yadda Ake Gwamnoni Ke Gusanar Da Zaben Kananan Hukumomi

by Muhammad
3 hours ago
0

Daga Ibrahim Muhammad, Cibiyar nazarin Damakwaradiyya dake karkashin jami'ar Bayero...

Next Post

Trump: Jaba Tsoma Baki A Bar Mi Ki

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version