Idris Umar">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Arewa Hausa Reporters Forum Ta Karrama Hamisu Malam

by Idris Umar
July 22, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Arewa Hausa Reporters Forum Ta Karrama Hamisu Malam
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A cikin makon daya gabata ne dandamalin masu yada labarai da harshen Hausa su ka karrama mataimaki shugaban kungiyar Yan gwari ta kasa a garin Danja da ke jihar Katsina.

Wakilinmu na daya daga cikin wakilan kafafafen yada labarai da su ka halacci taron a wannan rana.
Ga rahoton da ya aiko Mana dashi kamar haka:
Taron an gudanar da shi ne a bubban dakin taro na cibiyar koyar da ilmin shugabanta da zamantakewa da ke garin Kudan wato citizens an Leadership hall.
Bayan da manyan baki sarakuna da Yan siyasa daga bangarori daban daban har da mawaka su halar ta ne sai wanda ya jagoranci dandamalin kwamret U.I Samaru ya gabatar da jawabin makasudin da yasa Arewa Hausa Reporters Forum zasu karrama shi mataimakin kungiyar Yan gwari ta kasa wato Alhajin Hamisu Malam Danja a wannan rana.
Daga cikin bayanan kwamret I.U Samaru yace, mataimaki shugaban kungiyar Yan gwari ta kasa zai Sami karamcine bisa yadda bicike ya tabbatar cewa Yana da kishin ci gaban kasa a bangaren taimakawa matasa ta bangarori da dama na rayuwa.
Ya kara da cewa, Alhaji Hamisu Malam na daya daga cikin wanda su ka taimaka wajan tabbatar da kasuwar tumatur ta garin Danja ya wanzu Wanda a halin yanzu ake alfahari da ita a fadin Arewa da Afrika Baki daya.
Kwamret I.U Samaru yace wannan dabi’a ta Alhajin Hamisu Malam itace ake bukatar shugabanni su rinkayi a cikin jama’ar su yace farfado da kaduwar tumatur ta Danja ya kawo cigaba Mai yawa a bangarori da dama ciki har da taimakawa Gwamnati wajan samawa matasa abin yi da ya rage matsalar kalubalen tsaro a yanki.
Ya ce, hakan ne yasa Arewa Hausa Reporters Forum zata karrama Alhaji Hamisu Malam, a matsayin (Garkuwan Matasan Danja) don bashi kwarin guiwa.
Hahaji Yazid Sadik shine sarkin Fulanin Danja kuma shine Uban Taro a lokacin da ya ke nasa jawabin sai ya fara da godiya ga Allah madaukakin sarki kuma yayi sallati ga Annabin rahama Muhammad tsira da aminci su tabbatar a gareshi.
Bayan haka yayi jinjina ga Arewa Hausa Reporters Forum bisa kara da su ka nunawa karamar hukumar Danja da Jihar Katsina baki daya bisa karrama Danmu Alhaji Hamisu Malam mataimakin Shugaban karamar Yan Gwari na kasa baki daya yace, hakan ya zama darasi ne ga Yan baya da cewa ashe duk abin da mutum ya ke yi Jama’a na kallonsa! yace sunji dadi sosai Allah ya bar zumunci ya kuma mayar da kowa gida lafta
Shi ma kwamishinan lafiya na jihar Katsina Injiniya Yakubu Nuhu a nasa jawabin ya nuna jinjina ne ga Arewa Hausa Reporters Forum bisa karamta abokinsu da sukayi, kuma yayi fatan alheri tare da yi masu addu’a ta musamman bisa kokari da girmamawa da su ka nunawa abokin su a karamar hukumar Danja da jihar Katsina Mai tarin albarka.
Bayan Shugaban kungiyar Yangwari ta kasa Alaramma ya mika kambin karamcin ga Alhaji Hamisu Malam ne gurin ya dauki Tafi da cewa da jinjina na nuna farin ciki da wannan karamcin da yazo was jama’ar Danja da kungiyar Yan gwari na kasa baki daya.
Karshe sai Alhaji Hamisu Malam yayi jawabin godiya tare da fatan alheri ga Arewa Hausa Reporters Forum kuma yayi fatan alheri ga dukkan jama’ar da su ka zo don tayashi murna.
Daga cikin Mayan Baki akwai Alhaji Rabi’u Kugiya O.6 da sakataren Kungiya yan gwari na Danja sai Alhaji Yahaya Shehu Bakori da Hajiya Fatima Malunfashi da dai sauransu
An yi taro Lafiya an tashi lafiya.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Korona: Za A Raba Abincin Tallafin Bisa Adalci – Abdullahi Muhammad

Next Post

Na Yi Wa ’Yan Sanda 41,863 karin Girma Cikin Wata 18 – Adamu

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Idris Umar
2 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Idris Umar
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Idris Umar
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
shugaban rundunar yan sanda

Na Yi Wa ’Yan Sanda 41,863 karin Girma Cikin Wata 18 – Adamu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version