Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Arsenal Na Ci Gaba Da Zawarcin Zaha

by
2 years ago
in WASANNI
2 min read
Ana Barazanar Kashe Wilfred Zaha Na Crystal Palace
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Sabon kociyan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, Mikel Arteta, ya sake bayyana cewa akwai bukatar kungiyar ta sayo masa dan wasan gaba na Crystal Palace, Wilfred Zaha, dan kasar Ibory Coast, a watan Janairu mai kamawa.

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace dai ta bayyana wa Arsenal cewa idan har tana son sayan dan wasanta na gaba sai ta biya fam miliyan 80 idan kuma ba haka ba sai dai ta bar mata dan wasanta.

A farkon wannan kakar wasan ne dai dan wasan ya bayyana cewa ya shirya barin kungiyar domin bugawa a babbar kungiya duk da cewa ya taba zaman kungiyar kwallon kafa ta Manchester United amma zaman bai yi masa dadi ba a lokacin tsohon kociyan kungiyar, Sir Aled Ferguson.

Labarai Masu Nasaba

Chiellini Ya Bar Juventus

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

Kawo yanzu dai Arsenal ce kungiyar da ake ganin dan wasan mai shekara 26 a duniya zai koma kuma tuni ya roki shugabannin kungiyar dasu amince su fara Magana da Arsenal domin yasamu damar komawa babbar kungiya.

Sabon kociyan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal dai yana ganin zasu iya sayan dan wasan akan fam miliyan 55 sai dai Crystal Palace ta bayyana cewa baza ta sayar da dan wasan ba kasa da Fam miliyan 80 farashin da zaiyi wuya Arsenal ta iya biya a halin yanzu musamman a watan Janairu da wasanni sukayi nisa.

Crystal Palace tana bukatar fam miliayn 80 akan dan wasan wanda ya zura kwallaye 10 cikin wasanni 35 din daya buga a kakar wasan data gabata hakan zaisa Arsenal bazata iya biyan kudin ba bayan da kungiyar ta sayi Nicholas Pepe fam miliyan 72 a farkon wannan kakar.

Sai dai Arsenal zata iya kara samun wasu kudaden ta hanyar sayar da wasu daga cikin manyan ‘yan wasanta kuma tuni aka fara rade radin cewa ta amince zata sallamar da wasu daga cikin ‘yan wasanta da suka hada da Ozil da Dhaka da kuma Lucas Toreira.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Barcelona Tana Fatan Lautaro Martinez Ya Maye Gurbin Suares

Next Post

Ina Ya Kamata Na Kalla A Jikin  Budurwata ?

Labarai Masu Nasaba

Chiellini

Chiellini Ya Bar Juventus

by Abba Ibrahim Wada
10 hours ago
0

...

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

barcelona

Barcelona Ta Sa Hukumar La Liga Asarar Makudan Kudade

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

Next Post

Ina Ya Kamata Na Kalla A Jikin  Budurwata ?

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: