ASUU Ta Yi Kira Ga Majalisar Kasa Ta Cire TETfund Daga Tsarin Sabuwar Dokar Haraji
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ASUU Ta Yi Kira Ga Majalisar Kasa Ta Cire TETfund Daga Tsarin Sabuwar Dokar Haraji

byIdris Aliyu Daudawa and Sulaiman
10 months ago
Ilimi

Kungiyar Malaman Jami’oi ta kasa ta yi kira da Shugabannin majalisun dattawa da wakilai da cewar su dauki matakan da suka kamata wajen kare hukumar gidauniyar manyan makarantu (TETFund) daga cikin tsarin dokar samar da gyara a al’amuran haraji na shekarar 2024.

A wani jawabin data fitar ranar Jumma’a ta makon daya gabata wadda ke dauke da sa hannun Shugaban kungiyar na kasa,Farfesa Emmanuel Osodeke, ta yi kakkausar sukar cewar dokar idan aka amince da ita a yadda take, zata samar da cikas kan irin muhimmin taimakon da hukumar take badawa ta bangaren ci gaban ilimi.

  • Kudin Kirifto: An Cafke Dan Nijeriya Da Laifin Damfarar ‘Yan Australiya Dala Miliyan 8
  • Bangarorin Da Suka Fi Samun Kaso Mai Tsoka A Kasafin Kudin 2025

“Kungiyar ASUU tana sane da duk halin da ake ciki na maganganun da ake dangane da kawo gyara da samar da doka a tsarin haraji a Nijeriya a shekarar, 2024,wanda a yanzu lamarin yana gaban majalisun kasa.Daga cikin dokar haraji akwai maganar za ayi gyara a dokar harajin daya shafi ilimi kamar yadda lamarin yake,”.

Abin da akwai daure kai da ban takaici, domin kuwa sashi na 59 karamin sashi na(3)na dokar ya bayyana cewa kashi 50 na harajin ci gaba za a ba TETFund a shekarun 2025 da 2026 yayin da hukumomin NITDA,NASENL da NELFUND za su raba sauran kashi 50 da ya rage.

Kamar dai yadda lamarin ya ke cewar kungiyar ta ASUU, TETFund, za ta samu kashi “66.7 a shekarar 2027, 2028 da kuma 2029 na shekarun da ake gwada shi lamarin daga nan kuma gaba babu wani abu.

“ASUU ta damu kwarai dangane da wannan lamari mai hadari na sabuwar dokar haraji,da ake kira harajin ci gaba inda duk wasu tsare- tsaren TETFund za a maida su ga sabuwar hukuma mai suna gidauniyar bada bashin ilimi ta kasa (NELFUND).

“Gaskiyar lamarin shi ne a sanadiyar sabuwar dokar haraji idan har aka amince da ita abin yana nufin daga shekarar 2030, dukkan kudaden da aka samu da suna gidauniyar ci gaba za a rika tura sune zuwa hukumar NELFUND. ASUU tace shi abin ba ma kawai yana da ban takaici bane domin kuwa idan aka kalli ci gaban kasa akwai babbar matsalar da ita hukumar TETFund za ta shiga.

“ASUU ta ci gaba da bayani inda ta ce ba zata kame hannuwanta ba tana ganin ana kokarin kawo karshen ita hukumar TETfund, wadda ita ta kasance ne a matsayin abinda ya biyo bayan zaman da aka yi tsakanin ita kungiyar da gwamnatoci suka yi tun shekarar 1992. A namu ganin idan aka yi gyara a dokar da aka yi a shekarar 2011 ta TETFund, ko dai kawai don ana son ayi hakan ne saboda wani dalili, ba karamin ci baya bane ga lamarin daya shafi ilimi bane kadai, har ma Nijeriya a matsayin ta na kasa.

“Wannan shi yasa domin haka ne, ASUU tana kira majalisun kasa musamman ma Shubannnin majalisun dattawa da ta wakilai ta tarayya, su yi duk iyakar iyarsu su kare TETFund kada ayi amfani da dokar kawo gyara haraji ta 2024,har a kai ga samun damar tarwatsa ta kamar yadda sanarwar ta bayyana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version