Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta

byKhalid Idris Doya and Sulaiman
9 months ago
Bala Mohammed

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya naɗa uku daga cikin Kwamishinoni biyar da ya sallama daga muƙamansu a matsayin manyan masu ba shi shawara a ɓangarori daban-daban. 

 

Idan za ku tuna dai mun labarto cewa gwamnan da safiyar ranar Talata ya sallami Kwamishinonin guda biyar da suka haɗa da: Dakta Jamila Mohammed Dahiru – daga ma’aikatar ilimi; Barista Abubakar Abdulhameed Bununu – Tsoron Cikin Gida; Kwamared Usman Danturaki wanda aka kora a matsayin Kwamishinan watsa labarai; Farfesa Simon Madugu Yalams – Ayyukan Gona sai kuma Kwamishina a ma’aikatar harkokin addinai, Alhaji Yakubu Ibrahim Hamza

  • Hatsarin Kwale-kwale: Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya Ta Ceto Jami’an ‘Yansanda 8 Da Wani A Bayelsa
  • Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

Sai dai awannin da wannan matakin, gwamnan ya naɗa uku daga cikinsu a matsayin manyan Mashawarta domin su ci gaba da amfani da gogewarsu wajen taimaka wa gwamnatin jihar a ɓangaren gudanar da harkokin mulki.

 

Sabbin waɗanda gwamnan ya naɗa a matsayin manyan masu ba shi shawara sun ƙunshi, Hon. Abubakar Abdulhameed Bununu – babban mashawarci a ɓangaren haɗa kan jama’a da yankuna; Kwamared Usman Danturaki – mashawarci kan harkokin kwadago da shirin taimakekeniyar Fansho yayin da lima Farfesa Simon Madugu Yalams – Mashawarcin kan fasaha da ilimin koyon sana’ar hannu.

 

A wata sanarwar da mai magana da yawun gwamnan jihar, Mukhtar Mohammed Gidado ya fitar a daren ranar Talata, ya ce, naɗe-naɗen da suka fara aiki nan take an yi ne da nufin gwamnan na kyautata shugabanci da janyo kowa a jika haɗi da muradun cimma nasarori kan burikan gwamnati mai ci.

 

Gwamnan ya hori sabbin waɗanda ya naɗan da su yi amfani da gogewarsu da ƙwarewarsu wajen ba da tasu gudunmawar wajen cimma kyawawan ayyukan raya jihar. Kana, ya nemi su yi aiki tsakani da Allah domin kyautata rayuwar al’ummar jihar Bauchi.

 

Gwamnan ya jaddada aniyarsa na tabbatar da gaskiya da rikon amana hadi da gudanar da mulki na kowa da kowa domin ciyar da jihar zuwa gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version