Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Ayyuka: Jihar Filato Ta Amince Da Fitar Da Biliyan Uku Daga Yarjejeniyar Zuba Jari

by Khalid Idris Doya
February 1, 2021
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Sassauta Dokar Hana Fita
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Majalisar Zartaswar jihar Filato ta amince da fitar da naira biliyan uku (N3b) daga asusun ajiyar yarjejeniyar zuba jarin babban kasuwa domin gudanar da wasu manyan ayyukan raya jihar.

Wannan matakin na zuwa ne bayan zaman da majalisar ta yi a 2021 a ranar Juma’a karkashin jagorancin gwamnan jihar Simon Bako Lalong da ya gudana a gidan gwamnatin jihar ta Little Rayfied, Jos.
Kwamishinan yada labarai da sadarwa na jihar, Mista Dan Manjang; kwamishinan kudi na jihar, Dakta Misis Regina Soemlat da kuma kwamishinan kasuwanci da masana’antu, Misis Abe Aku su ne suka bada wannan bayanin na matsayar da suka dauka yayin da suke tsegunta wa ‘yan jarida kadan daga cikin matakan da zaman da suka aiwatar ya cimma.
Kwamishinan yada labaran, Dan Manjang, ya yi bayanin cewa amincewa da fitar da kudaden zai taimaka sosai wajen ganin an samu nasarar karasa wasu daga cikin muhimman ayyukan raya jihar da ake kan gudanar da su a halin yanzu.
Ya ce, bisa raguwar kason kudaden shiga na haraji da kuma raguwar adadin kaso-kaso da ake amsa daga asusun gwamnatin tarayya sakamakon annobar Korona, hakan ya sanya gwamnatin jihar daukan matakan da suka dace wajen ganin an samu kudade ta wasu hanyoyin domin ci gaba da aiwatar da ayyukan raya jihar da al’umman jihar.
Ita kuma kwamishinan kudi na jihar, Dakta Misis Regina Soemlat cewa ta yi, biliyan uku din na daga cikin bari ne na adadin kudi yaryeyeniyar zuba jari ta naira biliyan 30 da aka samar tun da fari ta tsarin kafa tarihin gwamna mai ci ta fuskacin zuba ayyukan raya jihar wato ‘Lalong Legacy Projects’.
A cewarta hakan zai bada damar kammala shirin kafa tarihi na gwamna mai ci na samun nasarar kammala ayyukan da ake gudanarwa a fadin jihar a halin yanzu.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Yanzu Tarbiyyar ’Ya’ya Ta Fi Karfin Iyaye Su Kadai – Dala

Next Post

Tsohon Dan Majalisar Lokoja, Hon Hashim, Ya Kwanta Dama

RelatedPosts

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

by Khalid Idris Doya
1 day ago
0

Daga Ahmed Muh'd Danasabe, Lokoja Ranar Lahadi da ta gabata...

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

by Khalid Idris Doya
1 day ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri Biyo bayan harin da mayakan Boko...

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

by Khalid Idris Doya
1 day ago
0

Daga Musa Muhammad, Abuja An kammala dukkan shirye-shirye don fara...

Next Post
Tsohon Dan Majalisar Lokoja, Hon Hashim, Ya Kwanta Dama

Tsohon Dan Majalisar Lokoja, Hon Hashim, Ya Kwanta Dama

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version